Home Labarai Gwamnatin Kano ta Musanta Kashe naira biliyan 10 a kayan Ofis

Gwamnatin Kano ta Musanta Kashe naira biliyan 10 a kayan Ofis

Gwamnatin jihar Kano ta musanta cewa ta kashe naira biliyan 10 wajen siyan kayayyakin Ofis cikin watanni uku na farkon shekara ta 2024.

wannan dai na kunshe ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar kano Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya sanyawa hannu kuma ya aikowa PRNigeria.

sanarwar ta ce ”Magana ta gaskiya labarin ba gaskiya ba ne, gaskiyar abun da muka kashe shi ne naira miliyan 596, don haka muna kira ga al’ummar jihar Kano da su yi watsi da labarin bashi da tushe ballantana makama”.

Idan za a iya tunawa a ranar laraba, jaridar “Sahara Reporters”, ta rawaito cewa gwamnatin jihar Kano ta kashe kimanin naira biliyan 10 wajen siyan kayan ofis.

”Ma’aikatar kasafi da tsare-tsare ta jihar kano ta fitar da rahoton yadda aka aiwatar da zangon farko na kasafin kudin jihar na bana a ranar 28 ga watan Yuli, 2024, babu shakka a adadin kudin da suka fitar akwai kuskure, amma ya kamata ayi musu uzuri saboda suma yan adam ne”. Inji Sanusi Bature

Ya ce matakin da gwamnatin Kano ta dauka na fitar da rahoton akan lokaci ya nuna yadda gwamnatin ta ke kokarin yin komai a bayyane ba tare da yin kunbiya-kunbiya ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp