Home Labarai Ta kashe mijinta mai cutar shanyewar ɓarin jiki, ta jefar da gawarsa...

Ta kashe mijinta mai cutar shanyewar ɓarin jiki, ta jefar da gawarsa a kango

Ana zargin wata mata mai suna Rahimat Salaum da kashe mijinta mai fama da larurar shanyewar ɓarin jiki sannan ta jefar da gawarsa a cikin wani kango.

Lamarin ya faru ne a yankin Pegi da ke Babban Birnin Tarayya Abuja.

Kakakin rundunar ’yan sanda ta shiyyar Abuja, SP Josephine Adeh, ita ce ta tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da yammacin Talata.

Ta ce tuni jami’an rundunar da ke yankin na Pegi ne suka cafke Rahimat a ranar Litinin.

A cewar Josephine, an kama matar ne lokacin da take ƙoƙarin tserewa da kayayyakin mijin nata, kafin ’yan sanda su yi mata ƙofar-rago su kama ta.

“Bayan an yi mata tambayoyi, wacce ake zargin ta amsa cewa ita ce ta kashe mijin nata bayan wata sa’insa da ta shiga tsakaninsu. Daga nan ne ta yi wa jami’anmu jagora zuwa kangon da ta jefar da gawar tasa, inda aka tarar da shi ya yi mummunar ƙonewa,” in ji Kakakin ’yan sandan.

Sai dai ta ce ’yan sanda na ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin, kuma da zarar sun kammala za su miƙa ta gaban kotu domin ta girbi abin da ta shuka.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp