Home Labarai Ta kashe mijinta mai cutar shanyewar ɓarin jiki, ta jefar da gawarsa...

Ta kashe mijinta mai cutar shanyewar ɓarin jiki, ta jefar da gawarsa a kango

Ana zargin wata mata mai suna Rahimat Salaum da kashe mijinta mai fama da larurar shanyewar ɓarin jiki sannan ta jefar da gawarsa a cikin wani kango.

Lamarin ya faru ne a yankin Pegi da ke Babban Birnin Tarayya Abuja.

Kakakin rundunar ’yan sanda ta shiyyar Abuja, SP Josephine Adeh, ita ce ta tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da yammacin Talata.

Ta ce tuni jami’an rundunar da ke yankin na Pegi ne suka cafke Rahimat a ranar Litinin.

A cewar Josephine, an kama matar ne lokacin da take ƙoƙarin tserewa da kayayyakin mijin nata, kafin ’yan sanda su yi mata ƙofar-rago su kama ta.

“Bayan an yi mata tambayoyi, wacce ake zargin ta amsa cewa ita ce ta kashe mijin nata bayan wata sa’insa da ta shiga tsakaninsu. Daga nan ne ta yi wa jami’anmu jagora zuwa kangon da ta jefar da gawar tasa, inda aka tarar da shi ya yi mummunar ƙonewa,” in ji Kakakin ’yan sandan.

Sai dai ta ce ’yan sanda na ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin, kuma da zarar sun kammala za su miƙa ta gaban kotu domin ta girbi abin da ta shuka.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp