Home Labarai ‘Yan majalisar wakilai a Nijeriya sun bukaci dakatar shugaban NNPC

‘Yan majalisar wakilai a Nijeriya sun bukaci dakatar shugaban NNPC

Ƴan majalisar wakilai 15 a ƙarkashin ƙungiyar The Economy Rescue Group”, sun nemi da a dakatar da shugaban rukunin kamfanin mai na Nijeriya Mele Kyari.

Ƙungiyar ta yi ikirarin cewa rashin tafiyar da tsare tsare karkashin jagorancin Kyari a NNPC ne ke jawo ƙalubalen da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke fuskanta.

Wannan na cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a Abuja kuma shugabanta ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Oredo, Esosa Iyawe, shi ne ya sanya mata hannu kuma aka saki a ranar Talata, inda ƙungiyar ta dage cewa a dakatar da Kyari har sai an samu sakamakon kwamitin hadin gwiwa na majalisar wakilai game da binciken kwakwaf da ake yi na kan harkokin man fetur game da halin da kamfanin mai na kasa ke ciki.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Mu ‘yan majalisa mai ɗauke da mutane 15 mun lura cewa ko shakka babu matsalolin da ake fuskanta a bangaren man fetur da iskar gas a gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya samo asali ne sakamakon gazawa da rashin gudanar da ayyukan hukumar ta NNPC a karkashin jagorancin Kyari. Don haka, don warware waɗannan matsaloli dole ne su yi murabus.

Haka kuma ƴan majalisar na zargin shugaban kamfanin na NNPC da sauran ma’aikatan gudanarwar da yi wa tsarin shugaban kasa na daidaita tattalin arziki mai lakabin “Renewed Hope Agenda” zagon kasa.
“Tunda sun kasa sauka da kansu, to bai kamata shugaban kasa ya yi kasa a gwiwa ba wajen dakatar da su har sai an gama gudanar da binciken da majalisar wakilai ke gudanarwa kan harkokin man fetur.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp