Home Labarai An dage dokar hana zirga-zirga a jihar Borno

An dage dokar hana zirga-zirga a jihar Borno

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya ɗage dokar taƙaita zirga-zirga da aka sanya a jihar, bayan fashewar bom a Kawori ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 16 tare da jikkata wasu.

Yayin da yake jawabi da aka yaɗa a kafofin yaɗa labaran jihar, Gwamna Zulum ya jajanta wa iyalan waɗanda suka mutu a harin na Kawori.

”Ina miƙa saƙon ta’aziyyar ga iyalan waɗanda harin ya shafa da kuma duka mutanen Borno, ina kuma jajanta wa waɗanda suka jikkata, waɗanda a yanzu haka ke asibiti suke kuma samun kulawar likitoci”.

Gwamnan ya kuma ce tun da farko an sanya dokar ne domin hana mayaƙan Boko Haram amfani da damar wajen haifar da tashin hankali a jihar.

Ya ƙara da cewa ɓata-gari ne suka yi shigar burta domin shiga cikin masu zanga-zangar lumana, inda suka yi yunƙurin kawo hargitsi, sai dai a cewarsa jami’an tsaro sun samu nasarar kwantar da hankula.

Yayin da yake bayyana janye dokar taƙaita zirga-zirgar, Gwamna Zulum ya ce mutane su fita harkokinsu, amma jami’an tsaro za su ci gaba da sanya idanu, domin magance duk wani abu da suka ga zai kawo tashin hankali.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp