Home Labarai Sojojin Nijeriya zasu dauki mataki muddin aka cigaba da barna a zanga-zanga...

Sojojin Nijeriya zasu dauki mataki muddin aka cigaba da barna a zanga-zanga – CDS

Rundunar sojin Nijeriya tace zata saka hannun muddin tashe tashen hankula suka cigaba da aukuwa a wasu jihohin kasar nan sakamakon zanga – zangar yaki da talauci da tsadar rayuwa.

Shugaban dakarun soji Janar Christopphare Musa ne yabbayan hakan, yayin da yake ganawa da manema labarai a birnin tarayya Abuja, inda yace dakarun sojoji zasu fita domin magance wasu tashe tashen hankula ta baranatar da dukiya dake faru a wasu sassan kasar nan.

Rahotannin sun bayyana cewa sakamakon zangar zangar ya haifar da mutuwar akalla mutane 17 a birnin Abuja, kano niger, Borno, Kaduna da kuma Jihar jigawa, inda aka balle bankuna wuraren kasuwanci, yayin da hanyoyi da dama aka lalata su.

A wasu sassan kasar nan zanga-zangar ta cigaba bayan da aka yi arangama tsakanin dakarun ‘yan sanda da masu zanga-zangar a fadin kasar nan.

Christopher yace suna sane da yunkurin Al’umma na yin zanga-zanga domin nuna bacin ransu kan tsadar rayuwar da suke ciki a fadin Nijeriya.

Daga bisani ya bukaci Al’ummar Nijeriya dasu hada kai, wajen kawar da kai da kuma haramtawa kan su daukar kayan mutane a yayin da kuma bayan zanga-zangar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp