Home Labarai Sojojin Nijeriya zasu dauki mataki muddin aka cigaba da barna a zanga-zanga...

Sojojin Nijeriya zasu dauki mataki muddin aka cigaba da barna a zanga-zanga – CDS

Rundunar sojin Nijeriya tace zata saka hannun muddin tashe tashen hankula suka cigaba da aukuwa a wasu jihohin kasar nan sakamakon zanga – zangar yaki da talauci da tsadar rayuwa.

Shugaban dakarun soji Janar Christopphare Musa ne yabbayan hakan, yayin da yake ganawa da manema labarai a birnin tarayya Abuja, inda yace dakarun sojoji zasu fita domin magance wasu tashe tashen hankula ta baranatar da dukiya dake faru a wasu sassan kasar nan.

Rahotannin sun bayyana cewa sakamakon zangar zangar ya haifar da mutuwar akalla mutane 17 a birnin Abuja, kano niger, Borno, Kaduna da kuma Jihar jigawa, inda aka balle bankuna wuraren kasuwanci, yayin da hanyoyi da dama aka lalata su.

A wasu sassan kasar nan zanga-zangar ta cigaba bayan da aka yi arangama tsakanin dakarun ‘yan sanda da masu zanga-zangar a fadin kasar nan.

Christopher yace suna sane da yunkurin Al’umma na yin zanga-zanga domin nuna bacin ransu kan tsadar rayuwar da suke ciki a fadin Nijeriya.

Daga bisani ya bukaci Al’ummar Nijeriya dasu hada kai, wajen kawar da kai da kuma haramtawa kan su daukar kayan mutane a yayin da kuma bayan zanga-zangar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp