Home Labarai Sojojin Nijeriya zasu dauki mataki muddin aka cigaba da barna a zanga-zanga...

Sojojin Nijeriya zasu dauki mataki muddin aka cigaba da barna a zanga-zanga – CDS

Rundunar sojin Nijeriya tace zata saka hannun muddin tashe tashen hankula suka cigaba da aukuwa a wasu jihohin kasar nan sakamakon zanga – zangar yaki da talauci da tsadar rayuwa.

Shugaban dakarun soji Janar Christopphare Musa ne yabbayan hakan, yayin da yake ganawa da manema labarai a birnin tarayya Abuja, inda yace dakarun sojoji zasu fita domin magance wasu tashe tashen hankula ta baranatar da dukiya dake faru a wasu sassan kasar nan.

Rahotannin sun bayyana cewa sakamakon zangar zangar ya haifar da mutuwar akalla mutane 17 a birnin Abuja, kano niger, Borno, Kaduna da kuma Jihar jigawa, inda aka balle bankuna wuraren kasuwanci, yayin da hanyoyi da dama aka lalata su.

A wasu sassan kasar nan zanga-zangar ta cigaba bayan da aka yi arangama tsakanin dakarun ‘yan sanda da masu zanga-zangar a fadin kasar nan.

Christopher yace suna sane da yunkurin Al’umma na yin zanga-zanga domin nuna bacin ransu kan tsadar rayuwar da suke ciki a fadin Nijeriya.

Daga bisani ya bukaci Al’ummar Nijeriya dasu hada kai, wajen kawar da kai da kuma haramtawa kan su daukar kayan mutane a yayin da kuma bayan zanga-zangar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp