Home Labarai An dage dokar hana zirga-zirga a jihar Borno

An dage dokar hana zirga-zirga a jihar Borno

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya ɗage dokar taƙaita zirga-zirga da aka sanya a jihar, bayan fashewar bom a Kawori ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 16 tare da jikkata wasu.

Yayin da yake jawabi da aka yaɗa a kafofin yaɗa labaran jihar, Gwamna Zulum ya jajanta wa iyalan waɗanda suka mutu a harin na Kawori.

”Ina miƙa saƙon ta’aziyyar ga iyalan waɗanda harin ya shafa da kuma duka mutanen Borno, ina kuma jajanta wa waɗanda suka jikkata, waɗanda a yanzu haka ke asibiti suke kuma samun kulawar likitoci”.

Gwamnan ya kuma ce tun da farko an sanya dokar ne domin hana mayaƙan Boko Haram amfani da damar wajen haifar da tashin hankali a jihar.

Ya ƙara da cewa ɓata-gari ne suka yi shigar burta domin shiga cikin masu zanga-zangar lumana, inda suka yi yunƙurin kawo hargitsi, sai dai a cewarsa jami’an tsaro sun samu nasarar kwantar da hankula.

Yayin da yake bayyana janye dokar taƙaita zirga-zirgar, Gwamna Zulum ya ce mutane su fita harkokinsu, amma jami’an tsaro za su ci gaba da sanya idanu, domin magance duk wani abu da suka ga zai kawo tashin hankali.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp