Home Labarai ‘Yan Sanda sun tarwatsa masu Zanga-Zanga a Birnin Abuja

‘Yan Sanda sun tarwatsa masu Zanga-Zanga a Birnin Abuja

Jami’an ‘yansanda sun harba hayaƙi mai sa hawaye kan masu zanga-zanga a filin wasa na MKO Abiola da ke birnin Abuja, domin tarwasu.

Masu zanga-zangar – waɗanda adadinsu bai kai yadda suka fito a ‘yan kwanakin bayan nan ba – sun taru a filin wasan domin ci gaba da gudanar da zanga-zangar.

Wasu matasan ƙasar ne dai suka shirya zanga-zangar da suka ce ta kwana 10 ne da nufin nuna adawa da matsin rayuwa da ake ciki.

To sai dai bayanai sun ce sa’o’i bayan fara zanga-zangar tasu sai ‘yansanda suka fara harba musu tiyagas da nufin tarwatsa su.

Hukumomin birnin Abuja ne dai suka ware filin wasan a matsayin wurin da za a gudanar da zanga-zangar, bayan umarnin wata kotu ta hana masu zanga-zangar zuwa wasu sassan birnin.

Ko a ranar Juma’a ma ‘yansandan sun harba wa masu zanga-zangar hayaƙi mai sa hawaye a shataletalen Berger da ke tsakiyar Abuja.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp