Home Labarai ‘Yan Sanda sun tarwatsa masu Zanga-Zanga a Birnin Abuja

‘Yan Sanda sun tarwatsa masu Zanga-Zanga a Birnin Abuja

Jami’an ‘yansanda sun harba hayaƙi mai sa hawaye kan masu zanga-zanga a filin wasa na MKO Abiola da ke birnin Abuja, domin tarwasu.

Masu zanga-zangar – waɗanda adadinsu bai kai yadda suka fito a ‘yan kwanakin bayan nan ba – sun taru a filin wasan domin ci gaba da gudanar da zanga-zangar.

Wasu matasan ƙasar ne dai suka shirya zanga-zangar da suka ce ta kwana 10 ne da nufin nuna adawa da matsin rayuwa da ake ciki.

To sai dai bayanai sun ce sa’o’i bayan fara zanga-zangar tasu sai ‘yansanda suka fara harba musu tiyagas da nufin tarwatsa su.

Hukumomin birnin Abuja ne dai suka ware filin wasan a matsayin wurin da za a gudanar da zanga-zangar, bayan umarnin wata kotu ta hana masu zanga-zangar zuwa wasu sassan birnin.

Ko a ranar Juma’a ma ‘yansandan sun harba wa masu zanga-zangar hayaƙi mai sa hawaye a shataletalen Berger da ke tsakiyar Abuja.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp