Home Labarai Tinubu yana kallon yadda ake gudanar da zanga-zanga a Nijeriya – Bagudu

Tinubu yana kallon yadda ake gudanar da zanga-zanga a Nijeriya – Bagudu

Shugaban kasa Bola Tinubu na kallon yadda zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa ke gudana a fadin kasar nan.

Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Atiku Bagudu ne ya bayyana hakan yayin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin din channels.

Zanga-zangar da ake yi a kasar nan na da nasaba da tsadar rayuwa, da tabarbarewar farashin Naira da kuma cire tallafin man fetur da gwamnatin Tinubu ta yi.

Ko da yake an yi ta kiraye-kirayen ga Tinubu ya yi jawabi ga al’ummar kasar bayan zanga-zangar ta shiga kwana na uku, amma har yanzu shugaba Tinubu bai yi hakan ba.

Sai dai Bagudu, ya ce shugaban na Nijeriya ya san halin da ake ciki sosai.

Kamar yada suma ministoci ke da nauyi a kan su, ya zame musu wajibi subi yada zanga-zangar ke gudana.

Ministan wanda ya amince da cewa ana shan wahala a kasar nan, amma gwamnatin tarayya na kokarin ganin an samu saukin rayuwa ga ‘yan kasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp