Home Labarai Jami’an tsaro sun yi arangama da masu Zanga-Zanga a jihar Kano

Jami’an tsaro sun yi arangama da masu Zanga-Zanga a jihar Kano

Wasu bayanai daga unguwar bachirawa a jihar Kano na bayyana cewa an yi arangama tsakanin matasan dake fakewa da zanga- zangar tsadar rayuwa suna fasa shaguna da dukiyoyin Al’umma a jihar da jami’an tsaro.

Matasan dai na kokarin kutsawa wani katafaren wurin sayar da kayan masarufi dana kwalam da makwalashe, wannan ne yasa dakarun ‘yan sandan daukar matakin dakile yunkurin nasu abinda ya kai ga harbin wasu daga cikin masu fakewa da zanga zangar.

Tun dai da sanyi safiya matasan suka fito domin sake dorawa daga inda aka tsaya a zangar da gwamnatin jihar ta dakatar da ita ta hanyar saka dokar hana fita, bayan ta zargi wasu manyan mutane a jihar da haifar da tarzoma a cikin ta.

Wakilin PRNigeria ya zaga yankin ya tattauna da wasu mutane da lamarin ya auku a gaban idon su, wanda suka ce har an sami asarar rayuka.

Mun yi kokarin tuntubar kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano Abdullahi Haruna Kiyawa domin jin yadda lamarin yake, amma bai sami damar amsa kiran ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp