Home Labarai Jami’an tsaro sun yi arangama da masu Zanga-Zanga a jihar Kano

Jami’an tsaro sun yi arangama da masu Zanga-Zanga a jihar Kano

Wasu bayanai daga unguwar bachirawa a jihar Kano na bayyana cewa an yi arangama tsakanin matasan dake fakewa da zanga- zangar tsadar rayuwa suna fasa shaguna da dukiyoyin Al’umma a jihar da jami’an tsaro.

Matasan dai na kokarin kutsawa wani katafaren wurin sayar da kayan masarufi dana kwalam da makwalashe, wannan ne yasa dakarun ‘yan sandan daukar matakin dakile yunkurin nasu abinda ya kai ga harbin wasu daga cikin masu fakewa da zanga zangar.

Tun dai da sanyi safiya matasan suka fito domin sake dorawa daga inda aka tsaya a zangar da gwamnatin jihar ta dakatar da ita ta hanyar saka dokar hana fita, bayan ta zargi wasu manyan mutane a jihar da haifar da tarzoma a cikin ta.

Wakilin PRNigeria ya zaga yankin ya tattauna da wasu mutane da lamarin ya auku a gaban idon su, wanda suka ce har an sami asarar rayuka.

Mun yi kokarin tuntubar kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano Abdullahi Haruna Kiyawa domin jin yadda lamarin yake, amma bai sami damar amsa kiran ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp