Ana fargabar mutuwar Mutane 16 sakamakon kifewar kwale-kwale a jihar Sokoto

Akalla mutane  16 ne suka ake zargin sun mutu bayan wani kwale-kwale makre da mutane ya kife a jihar sokoto dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Dundaye inda hukumar agajin gaggauwa ta NEMA ta bayyana cewa akwai mutane 19 da suka tsira da rayukansu.

Kwale-kwalen na ɗauke da manoma ne inda zai kai su gonakinsu na shinkafa a ranar Lahadi.

An gano gawa guda, sannan kuma akwai mata da yara daga cikin waɗanda suka ɓace.

Masu ninƙaya da kuma masu kamun kifi na cikin waɗanda suka shiga aikin ceton.

Jami’ai sun ce jirgin ya ɗauko ninkin mutanen da ya kamata ya ɗauka ne.

A makon daya wuce ma wasu manoma 15 sun nitse bayan jirgin ruwan da ya ɗauko su ya kife a jihar Jigawa da ke arewacin Nijeriya.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 35 minutes 18 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 16 minutes 43 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com