Home Labarai Tinubu yana iya bakin kokarinsa – T Gwarzo

Tinubu yana iya bakin kokarinsa – T Gwarzo

Karamin ministan gidaje da raya birane na Nigeria Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo ya tabbatarwa ‘yan Najeriya cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu yana bakin kokarinsa wajen gyara matsalolin kasar.

Ministan ya bada wannan tabbacin ne a lokacin da ya karbi bakuncin mambobin kungiyar APC 4G Forum na Kano da suka kai masa ziyarar ban girma a ofishin sa.

Ya bayyana cewa a halin yanzu shugaban kasar ya kaddamar da ayyuka da dama wadanda aka samar da su da niyya magance matsalolin da ke addabar al’umma.

Minista Gwarzo ya yi kira ga ’ya’yan kungiyar APC 4G Forum na Kano da su tabbatar da hadin kan jam’iyyar tare da bayar da gagarumar gudunmuwa don samun nasarar Shugaba Bola Ahmad Tinubu a yunkurinsa na sake dawo da kasar nan kan saiti.

Ya kuma shawarci kungiyar da ta hada kan dukkan ‘ya’yan jam’iyyar karkashin inuwa daya domin gujewa maimaita kurakuran da aka yi a baya. Ya kara da cewa ya kamata kowa ya tashi tsaye domin tallata gwamnatin Bola Tinubu.

Tun da farko, Shugaban rikon kungiyar APC 4G Forum na Kano, Kwamared Sale Jeli (Sarkin Fadar Karaye) ya bayyana nagartar Ministan, inda ya bayyana shi a matsayin jagora na gari mai kishin kasa, wanda a kodayaushe ya ba da fifiko wajen yi wa al’ummarsa hidima.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp