Home Labarai Mayakan Boko haram 44 sun mika wuya a jihar Borno

Mayakan Boko haram 44 sun mika wuya a jihar Borno

Dakarun rundunar sojin Nijeriya ta sami nasarar hallaka ýan ta’addan masu yawa, yayin da da dama suka mika wuya ga dakarun, haka kuma sun sami nasarar kwato Bindugu, alburusai, bama-bamai, da kuma garken shanu, gami da kama wadanda ake zargin ‘yan ta’addan ne a wani samume da suka kai.

Ta cikin wata sanarwa da PRNigeria ta samu rundunar ta ce a ranar 12 ga watan agustan 2024, ta kai wani simame a maboyar mayakan kungiyar tayar da kayar baya na boko haram tsagin ISWAP a karamara hukumar Bama dake jihar Borno a Arewa maso gabashin kasar.

Inda dakarun ta suka sami nasarar bindigar kakkabo jirgin sama ta (RPG) bama-bamai, bindugu guda biyu kirar gida, kwanson alburushi bindiga kira AK47, Babura guda 6 da kuma wasu magunguna kala-kala.

Haka kuma ayankin na arewa maso gabashi wasu mayakn boko haram 44 da iyalansu sun mika wuya a kananan hukumomin Dikwa da Gwoza dukka a jihar ta Borno.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp