Home Labarai Mayakan Boko haram 44 sun mika wuya a jihar Borno

Mayakan Boko haram 44 sun mika wuya a jihar Borno

Dakarun rundunar sojin Nijeriya ta sami nasarar hallaka ýan ta’addan masu yawa, yayin da da dama suka mika wuya ga dakarun, haka kuma sun sami nasarar kwato Bindugu, alburusai, bama-bamai, da kuma garken shanu, gami da kama wadanda ake zargin ‘yan ta’addan ne a wani samume da suka kai.

Ta cikin wata sanarwa da PRNigeria ta samu rundunar ta ce a ranar 12 ga watan agustan 2024, ta kai wani simame a maboyar mayakan kungiyar tayar da kayar baya na boko haram tsagin ISWAP a karamara hukumar Bama dake jihar Borno a Arewa maso gabashin kasar.

Inda dakarun ta suka sami nasarar bindigar kakkabo jirgin sama ta (RPG) bama-bamai, bindugu guda biyu kirar gida, kwanson alburushi bindiga kira AK47, Babura guda 6 da kuma wasu magunguna kala-kala.

Haka kuma ayankin na arewa maso gabashi wasu mayakn boko haram 44 da iyalansu sun mika wuya a kananan hukumomin Dikwa da Gwoza dukka a jihar ta Borno.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp