Home Labarai Gwamnatin Kano ta janye dokar hana fita gaba daya a jihar

Gwamnatin Kano ta janye dokar hana fita gaba daya a jihar

Gwamnan jihar Kano ya sanar da janye dokar hana fita da ya saka sakamakon tarzomar da ta biyo bayan zanga-zanga kan matsin rayuwa a Nijeriya.

Abba Kabir Yusuf ya sanar da matakin ne yayin da yake yi wa ‘yanjarida jawabi a jihar yau Litinin bayan wata ziyarara gani da ido da ya kai harabar kotun da matasa suka yi barna a ranar zanga-zangar.

“Gwamnati ta janye wannan doka gaba ɗaya, kuma mai girma gwamna ya jinjina wa malamai da jami’an tsaro da suka jajirce don ganin an samu zaman lafiya,” kamar yadda Kwamashinan Yaɗa Labarai Baba Halilu Dantiye ya shaida wa manema labarai cikin wani saƙon murya.

Gwamnati ta saka dokar a ranar 1 ga watan Agusta bayan wasu ɓata-gari sun auka wa gine-gine da shagunan mutane tare da yin wawashe kayayyaki a ranar farko ta zanga-zangar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp