Home Labarai Tinubu yana iya bakin kokarinsa – T Gwarzo

Tinubu yana iya bakin kokarinsa – T Gwarzo

Karamin ministan gidaje da raya birane na Nigeria Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo ya tabbatarwa ‘yan Najeriya cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu yana bakin kokarinsa wajen gyara matsalolin kasar.

Ministan ya bada wannan tabbacin ne a lokacin da ya karbi bakuncin mambobin kungiyar APC 4G Forum na Kano da suka kai masa ziyarar ban girma a ofishin sa.

Ya bayyana cewa a halin yanzu shugaban kasar ya kaddamar da ayyuka da dama wadanda aka samar da su da niyya magance matsalolin da ke addabar al’umma.

Minista Gwarzo ya yi kira ga ’ya’yan kungiyar APC 4G Forum na Kano da su tabbatar da hadin kan jam’iyyar tare da bayar da gagarumar gudunmuwa don samun nasarar Shugaba Bola Ahmad Tinubu a yunkurinsa na sake dawo da kasar nan kan saiti.

Ya kuma shawarci kungiyar da ta hada kan dukkan ‘ya’yan jam’iyyar karkashin inuwa daya domin gujewa maimaita kurakuran da aka yi a baya. Ya kara da cewa ya kamata kowa ya tashi tsaye domin tallata gwamnatin Bola Tinubu.

Tun da farko, Shugaban rikon kungiyar APC 4G Forum na Kano, Kwamared Sale Jeli (Sarkin Fadar Karaye) ya bayyana nagartar Ministan, inda ya bayyana shi a matsayin jagora na gari mai kishin kasa, wanda a kodayaushe ya ba da fifiko wajen yi wa al’ummarsa hidima.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp