Home Labarai NNPCL ya bankaɗo haramtattun matatun mai 63 a Najeriya

NNPCL ya bankaɗo haramtattun matatun mai 63 a Najeriya

Babban kamfanin man fetur na Najeriya NNPCL, ya ce ya bankaɗo wuraren 63 da ake tace mai fetur ba bisa ƙa’ida ba a cikin makon da ya gabata.

Cikin wani rahoton kamfanin da aka yaɗa a gidan Talbijin na ƙasar NTA, ya nuna cewa an gano haramtattun bututan mai 19 da kuma wurare 63 da ake tace mai ba bisa ƙa’ida ba.

Rahoton kamfanin na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da nuna damuwa kan jinkirin fara aikin matatar mai ta birnin Fatakwal, ba kamar yadda aka tsara tun farko ba.

Matatar ta Fatakwal – da ke ƙarƙashin kamfanin NNPCL – ta kasa fara aiki bayan an ɗage lokacin fara aikin nasa har sau shida.

Ma’aikatar albarkatun man fetur ta Najeriya da kamfanin mai na NNPCL sun alƙawarta fara aikin matatar cikin wannan wata, to sai dai alamu na nuna cewa ba lallai ne matatar ta fara tace man cikin wannan wata ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp