Home Labarai Farashin kayan abinci ya sauka a Nijeriya

Farashin kayan abinci ya sauka a Nijeriya

Hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta sanar a ranar Alhamis cewa, farashin kaya a ƙasar ya sauka a karon farko da kashi 33.4 cikin 100 a watan Yuli inda aka kwatanta da kashi 34.19 cikin 100 a watan Yunin shekarar da muke ciki.

Kayayyakin da farashin nasu ya sauka sun haɗa da shinkafa da masara da ƙwai da burodi da man fetur.

To sai dai kuma farashin makamashi na ci gaba da hauhawa a cikin shekara ɗaya da ta wuce a cewar hukumar.

Najeriya dai ta fara aiwatar da manufofin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasar tun a bara.

Ƙasar ta dauki matakai kamar cire tallafin man fetur da kuma farfaɗo da darajar kuɗin ƙasar, naira.

Shugaba ƙasar Bola Tinubu ya ce sauye-sauyen na da matukar muhimmanci kuma ya zama dole da nufin farfaɗo da tattalin arziƙin.

A farkon watan Augusta ne ƴan kasar suka gudanar da zanga-zanga a kan matsin rayuwa ta kwana 10 don matsawa gwamnati ɗaukar matakan sassauta al’amura.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp