Home Labarai NNPCL ya bankaɗo haramtattun matatun mai 63 a Najeriya

NNPCL ya bankaɗo haramtattun matatun mai 63 a Najeriya

Babban kamfanin man fetur na Najeriya NNPCL, ya ce ya bankaɗo wuraren 63 da ake tace mai fetur ba bisa ƙa’ida ba a cikin makon da ya gabata.

Cikin wani rahoton kamfanin da aka yaɗa a gidan Talbijin na ƙasar NTA, ya nuna cewa an gano haramtattun bututan mai 19 da kuma wurare 63 da ake tace mai ba bisa ƙa’ida ba.

Rahoton kamfanin na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da nuna damuwa kan jinkirin fara aikin matatar mai ta birnin Fatakwal, ba kamar yadda aka tsara tun farko ba.

Matatar ta Fatakwal – da ke ƙarƙashin kamfanin NNPCL – ta kasa fara aiki bayan an ɗage lokacin fara aikin nasa har sau shida.

Ma’aikatar albarkatun man fetur ta Najeriya da kamfanin mai na NNPCL sun alƙawarta fara aikin matatar cikin wannan wata, to sai dai alamu na nuna cewa ba lallai ne matatar ta fara tace man cikin wannan wata ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp