Home Labarai Ambaliyar ruwa ta rusa gidaje sama da budu 32 a Nijeriya

Ambaliyar ruwa ta rusa gidaje sama da budu 32 a Nijeriya

Hukumar bada agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA tace ambaliyar ruwa ta shafi mutane 227,494, inda ta lalata gidaje 32,837 a jihohi 27 dake fadin kasar.

Haka kuma sanarwa da NEMA ta fitar tace ambaliyar ta lalata kadada kimanin 16,488 na gonaki da tuni sun fara fitar da amfani

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin hukumar Ezekiel Manzo ya fitar a ranar Alhamis a birnin tarayya Abuja, sanarwar ta ambaci babban daraktan hukumar, Zubairu Umar na cewa hukumar zata cigaba da sanya idanu da kuma wayar da kan al’ummar kan matsalolin toshe magudanan ruwa da hanyoyin wucewar sa.

Umar ya shawarwa hukumar bayar da agajin gaggawar ta jihohi da shuwagabannin al’umma da su shiryawa daukar mataki kan samun yawaitar abaliyar ruwan anan gaba, sannan kuma ya ce kada manoma su damu bisa kamfar rashin ruwa, zai zo karshe kamar yadda hasashen NiMet ya bayyana.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp