Home Labarai NNPCL ya bawa ‘Yan Nijeriya hakuri kan karancin Man fetur

NNPCL ya bawa ‘Yan Nijeriya hakuri kan karancin Man fetur

Kamfanin mai na Nigeria NNPC ya ce ya damu matuka bisa yadda ake fuskantar karancin man fetur a wasu sassan Nigeria.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da babban jami’in sadarwa na kamfanin Olufemi Sonete ya fitar wadda aka raba manema labarai.

Ta cikin sanarwar NNPCL ya danganta matsalar da kalubalen aiki rarraba man fetur din a fadin kasar.

Haka kuma sanarwar tace NNPCL yana kira ga masu ababen hawa da su kara hakuri, yana aiki ba dare ba rana tare da masu ruwa da tsaki don shawo kan matsalar.

Al’ummar wasu sassan Nijeriya dai na fuskantar ƙarancin man fetur wanda hakan ya sanya ake sayar da man daga kan Naira 800 har yanzu Naira 950.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp