Home Labarai NNPCL ya bawa ‘Yan Nijeriya hakuri kan karancin Man fetur

NNPCL ya bawa ‘Yan Nijeriya hakuri kan karancin Man fetur

Kamfanin mai na Nigeria NNPC ya ce ya damu matuka bisa yadda ake fuskantar karancin man fetur a wasu sassan Nigeria.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da babban jami’in sadarwa na kamfanin Olufemi Sonete ya fitar wadda aka raba manema labarai.

Ta cikin sanarwar NNPCL ya danganta matsalar da kalubalen aiki rarraba man fetur din a fadin kasar.

Haka kuma sanarwar tace NNPCL yana kira ga masu ababen hawa da su kara hakuri, yana aiki ba dare ba rana tare da masu ruwa da tsaki don shawo kan matsalar.

Al’ummar wasu sassan Nijeriya dai na fuskantar ƙarancin man fetur wanda hakan ya sanya ake sayar da man daga kan Naira 800 har yanzu Naira 950.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp