Home Labarai Amnesty International ta magantu kan dambarwar NLC da Gwamnatin Nijeriya

Amnesty International ta magantu kan dambarwar NLC da Gwamnatin Nijeriya

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International a Najeriya ta nuna damuwa kan sabbin zarge-zargen taimaka wa ta’addanci da hukumomin kasar ke yi kan ƙungiyar ƙwadago ta NLC da shugabanninta.

A cikin wata takardar sanarwa da ta fitar, Amnesty ta soki yunkurin hukumomin gwamnati da cewa matakin da rundunar ƴansandan Najeriya ta ɗauka na gayyatar Joe Ajaero wani yunƙuri ne kawai na tursasa wa NLC ta yi abin da gwamnati ke so.

A ranar Talata ne wata sanarwa da rundunar ƴansanda ta Najeriya ta fitar ta buƙaci shugaban na NLC, Joe Ajaero ya bayyana a gabanta domin amsa tambayoyi kan wasu tuhume-tuhume da ake masa da suka shafi tallafa wa yunƙurin tayar da rikici a Najeriya.

Hakan na zuwa ne bayan wani samame da jami’an tsaro suka kai a hedikwatar ƙungiyar ta NLC, inda suka ce sun yi hakan ne a wani ɓangare na binciken da suke gudanarwa kan wani mai shirya tarzoma.

Amnesty International ta buƙaci hukumomin da su mutunta ƴancin ƙungiyoyin ƙwadago domin bayyana ra’ayoyinsu, ya kuma yi gargaɗin a guji amfani da ikon gwamnati wajen rufe bakin kungiyar ta NLC.

Amnesty International ta bayyana yadda ake samun karuwar cin zarafin ƙungiyar ƙwadagon a cikin shekarar da ta gabata, ciki har da harin da ƴansanda suka kai wa Ajaero a watan Nuwamba da wani samame da aka kai hedikwatar ta NLC a baya-bayan nan.

Kungiyar ta yi Allah-wadai da waɗannan ayyuka a matsayin katsalandan ga ƴancin kai na ƙungiyar ƙwadagon.

Amnesty ta kuma yi kira da a gaggauta kawo ƙarshen neman murƙushe shugabannin ƙungiyar ta NLC, tare da bayyana zargin da ake yi musu a matsayin maras tushe.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp