Home Labarai NLC na tattaunawa kan gayyatar da ‘yan sandan suka yiwa Ajaero

NLC na tattaunawa kan gayyatar da ‘yan sandan suka yiwa Ajaero

Manyan jagororin ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya NLC da suka hada da shugabanta, Joe Ajaero, sun hallara a hedikwatar ƙungiyar ta NLC domin gudanar da wani taron gaggawa na shugabannin ƙungiyar.

Taron ya biyo bayan sammacin da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta yi wa Ajaero na ya gurfana a gabanta domin amsa tambayoyi kan zarge-zargen da suka shafi samar da kuɗaɗe ga ayyukan ta’addanci, da cin amanar kasa, da kuma aikata laifuka ta shafukan intanet.

Umarnin ‘yan sanda dai ya buƙaci Ajaero ya gabatar da kansa da misalin karfe 10:00 na safiyar yau Talata domin amsa tambayoyi.

A ranar Litinin ne aka gayyaci Ajaero ta hanyar wata wasiƙa mai dauke da sa hannun ACP Adamu Muazu a madadin mataimakin kwamishinan ƴansanda mai kula da ɓangaren tattara bayanan sirri.

ko dai a makwannin da suka gabata dakarun ‘yan sandan sun kutsa kai ofishin kungiyar dake birnin tarayya Abuja, inda kungiyar ta yi zargin sun yi mata barna a wajen adana litattafan ta gami da tilastawa masu gadi sai sun basu mukullan ofisoshin dake hawa na biyu na ginin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp