Home Labarai Jihar Kano ta sake rabauta da mukami a mulkin Tinubu

Jihar Kano ta sake rabauta da mukami a mulkin Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin Farfesa Abdullahi Saleh Usman a matsayin shugaban hukumar kula da alhazai ta Nigeria (NAHCON).

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Farfesa Abdullahi Sale fitaccen malamin Addinin musulunci ne wanda ya yi digirinsa na farko a cibiyoyin ilimi na Musulunci guda biyu – Jami’ar Madina da Jami’ar Peshawar da ke Pakistan.

Ya kuma kware wajen gudanar da aikin Hajji, inda ya taba rike mukamin Shugaban Hukumar Jin dadin Alhazai ta Jihar Kano, kuma ya samu nasarar mai tarin yawa a lokacinsa.

Sabon mukamin nasa zai fara aiki ne bayan Majalisar kasa ta amince da nadin.

Shugaban ƙasar ya yiwa sabon shugaban hukumar ta NAHCON fatan alkhairi tare da fatan zai gudanar da aikinsa bisa gaskiya da rikon amana ga alhazan Nigeria .

Idan dai za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito ana zargin tsohon shugaban hukumar ta NAHCON Jalal Arabi da almundahanar kudade bayan kammala ibadar aikin hajjin bana.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp