Home Labarai Jihar Kano ta sake rabauta da mukami a mulkin Tinubu

Jihar Kano ta sake rabauta da mukami a mulkin Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin Farfesa Abdullahi Saleh Usman a matsayin shugaban hukumar kula da alhazai ta Nigeria (NAHCON).

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Farfesa Abdullahi Sale fitaccen malamin Addinin musulunci ne wanda ya yi digirinsa na farko a cibiyoyin ilimi na Musulunci guda biyu – Jami’ar Madina da Jami’ar Peshawar da ke Pakistan.

Ya kuma kware wajen gudanar da aikin Hajji, inda ya taba rike mukamin Shugaban Hukumar Jin dadin Alhazai ta Jihar Kano, kuma ya samu nasarar mai tarin yawa a lokacinsa.

Sabon mukamin nasa zai fara aiki ne bayan Majalisar kasa ta amince da nadin.

Shugaban ƙasar ya yiwa sabon shugaban hukumar ta NAHCON fatan alkhairi tare da fatan zai gudanar da aikinsa bisa gaskiya da rikon amana ga alhazan Nigeria .

Idan dai za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito ana zargin tsohon shugaban hukumar ta NAHCON Jalal Arabi da almundahanar kudade bayan kammala ibadar aikin hajjin bana.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp