Home Labarai Amnesty International ta magantu kan dambarwar NLC da Gwamnatin Nijeriya

Amnesty International ta magantu kan dambarwar NLC da Gwamnatin Nijeriya

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International a Najeriya ta nuna damuwa kan sabbin zarge-zargen taimaka wa ta’addanci da hukumomin kasar ke yi kan ƙungiyar ƙwadago ta NLC da shugabanninta.

A cikin wata takardar sanarwa da ta fitar, Amnesty ta soki yunkurin hukumomin gwamnati da cewa matakin da rundunar ƴansandan Najeriya ta ɗauka na gayyatar Joe Ajaero wani yunƙuri ne kawai na tursasa wa NLC ta yi abin da gwamnati ke so.

A ranar Talata ne wata sanarwa da rundunar ƴansanda ta Najeriya ta fitar ta buƙaci shugaban na NLC, Joe Ajaero ya bayyana a gabanta domin amsa tambayoyi kan wasu tuhume-tuhume da ake masa da suka shafi tallafa wa yunƙurin tayar da rikici a Najeriya.

Hakan na zuwa ne bayan wani samame da jami’an tsaro suka kai a hedikwatar ƙungiyar ta NLC, inda suka ce sun yi hakan ne a wani ɓangare na binciken da suke gudanarwa kan wani mai shirya tarzoma.

Amnesty International ta buƙaci hukumomin da su mutunta ƴancin ƙungiyoyin ƙwadago domin bayyana ra’ayoyinsu, ya kuma yi gargaɗin a guji amfani da ikon gwamnati wajen rufe bakin kungiyar ta NLC.

Amnesty International ta bayyana yadda ake samun karuwar cin zarafin ƙungiyar ƙwadagon a cikin shekarar da ta gabata, ciki har da harin da ƴansanda suka kai wa Ajaero a watan Nuwamba da wani samame da aka kai hedikwatar ta NLC a baya-bayan nan.

Kungiyar ta yi Allah-wadai da waɗannan ayyuka a matsayin katsalandan ga ƴancin kai na ƙungiyar ƙwadagon.

Amnesty ta kuma yi kira da a gaggauta kawo ƙarshen neman murƙushe shugabannin ƙungiyar ta NLC, tare da bayyana zargin da ake yi musu a matsayin maras tushe.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp