Home Labarai Sojojin Nijeriya zasu gudanar da bincike kan abin ya faru a Kaduna

Sojojin Nijeriya zasu gudanar da bincike kan abin ya faru a Kaduna

Babban hafsan sojin ƙasa na Nijeriya, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin da ya faru a kasuwar Sabon Birni da ke jihar KAduna domin gano haƙianin abinda ya faru, da kuma kamo wadanda ake zargi.

Cikin wani bidiyo da aka yaɗa a shafukan sada zumunta, an ga yadda wasu da aka yi zargin sojoji ne sun kashe mutum uku tare da shanu a ƙalla 100 a kasuwar Sabon Birni da ke yankin ƙaramar hukumar Igabi a jhar Kaduna.

To sai dai cikin wata sanarwa da rundunar sojin ƙasa ta Nijeriya ta fitar ta hannun daraktan yaɗa labaranta, Onyema Nwachukwu, ta jajanta wa iyalan al’ummar yankin Sabon Birni da mutanen da lamarin ya shafa, tare da alƙawarta gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

”Kuma duk jami’in da muka samu da hannu a wannan lamarin, to za mu ɗauki matakin da ya dace a kansa”, kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

Sanarwar ta ci gaba da cewa kundin tsarin mulkin Najeriya ya ɗora wa rundunar sojin ƙasa ta Najeriya alhakin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, don haka ba za ta lamunci duk wani yunƙurin saɓanin hakan ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp