Home Labarai Tinubu ya kadu da labarin mutuwar sarkin Gobir

Tinubu ya kadu da labarin mutuwar sarkin Gobir

Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinubu ya ce yayi matukar kaduwa da jin yadda yan bindiga suka kashe sarkin Gobir,tare da cin alwashin daukar mataki akan masu garkuwa.

A cikin sanarwar da mai Magana da yawun shugaban Najeriya Ajuri Ngelele ya fitar, ya ce shugaban ya bayyana kisan basaraken a matsayin cin zarafi da kuma tozarci da bazai bari a cigaba da aikawa ba.

Ya kumayi ta’aziyya ga iyalan marigayin, da masarautar Gobir da ma gwamnatin Sokoto.

Ya kuma yiwa ‘yan Najeriya albishir da cewar gwamnatinsa a shirye take wajan yakin ayyukan ‘yan ta’addah.

shugaban ya bayyana cewar yana yin duk mai yuwuwa wajan ganin ya tabbatar da tsaro a kasar, sai ‘yan siyasa da al’ummar kasar na cigaba da bayyana takaicin su gane da rashin tsaro da yafi kamari a yankin arewacin kasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp