Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinubu ya ce yayi matukar kaduwa da jin yadda yan bindiga suka kashe sarkin Gobir,tare da cin alwashin daukar mataki akan masu garkuwa.
A cikin sanarwar da mai Magana da yawun shugaban Najeriya Ajuri Ngelele ya fitar, ya ce shugaban ya bayyana kisan basaraken a matsayin cin zarafi da kuma tozarci da bazai bari a cigaba da aikawa ba.
Read Also:
- Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar Shekara
- Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci
- Binciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?
Ya kumayi ta’aziyya ga iyalan marigayin, da masarautar Gobir da ma gwamnatin Sokoto.
Ya kuma yiwa ‘yan Najeriya albishir da cewar gwamnatinsa a shirye take wajan yakin ayyukan ‘yan ta’addah.
shugaban ya bayyana cewar yana yin duk mai yuwuwa wajan ganin ya tabbatar da tsaro a kasar, sai ‘yan siyasa da al’ummar kasar na cigaba da bayyana takaicin su gane da rashin tsaro da yafi kamari a yankin arewacin kasar.












