Babban mai shari’a na ƙasa na 22, Olukayode Ariwoola ya yi ritaya a matsayin Alkalan Alkalan Nijeriya bayan cika shekarun aiki na shekara 70.
Ariwoola, wanda aka haife shi a ranar 22 ga watan Agusta a 1954, ritayar tasa ta kawo karshen aikin da ya shafe shekaru yana yi a fannin shari’a.
Read Also:
- Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar Shekara
- Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci
- Binciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?
A ranar 22 ga watan Nuwamba na 2011 ne aka nada mai shari’a Ariwoola a matsayin alkalin kotun koli , sannan ya sama babban mai shari’a na Nijeriya a 27 ga watan Yuni na 2022 bayan ajiye aikin da mai shari’a Tanko Muhammad yayi.
A ranar 21 ga watan Satumba na 2022, majalisar dattawa ta tabbatar da shi a matsayin babban alkalin Nijeriya.
Anasa rai dai, Kudirat Kekere-Ekun ce za ta gaje shi bayan majalisar shari’a ta kasa NJC, ta bada shawarar nada ta a mukamin.












