Hukumomi a Jamhuriyar Nijar, na gudanar da bincike kan wasu mutane biyu da ake zargin sun kamu da cutar ƙyandar biri a yankin Zinder.
Read Also:
- Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar Shekara
- Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci
- Binciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?
Babban magatakarda a ma’aikatar lafiyar Nijar Dakta Malam Ekoye Saidou wanda ya tabbatar da matakin cikin wata sanarwa ranar Laraba, ya buƙaci masu ruwa da tsaki a kowane mataki da su ƙarfafa matakan taka tsantsan a duk wuraren kiwon lafiya na gwamnati da masu zaman kansu da kan iyakoki.
Sanarwar tace ɗaukar matakin ya zama dole, sakamakon yadda cutar ta fara yaɗuwa zuwa yammacin Afirka.
Daga ranar 14 ga watan Agusta, mutane 833 ne suka kamu da cutar, ciki har da 9 da su ka mutu a yankin, wato 11 a Najeriya, 1 Ivory Coast da kuma 3 a Benin.












