Home Labarai Tinubu na neman mallaka wa kansa Nijeriya – Atiku

Tinubu na neman mallaka wa kansa Nijeriya – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, ya zargi shugaban ƙasar, Bola Tinubu da ‘neman mayar da Najeriya mallakin kansa’.

Atiku, ɗan takarar jam’iyyar PDP a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023 ya yi iƙirarin cewa Tinubu yana jinginar da makoman matasan Nijeriya ga kansa da iyalinsa da kuma abokansa na kusa.

Atiku ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe ya fitar a ranar Laraba, inda ya bayyana damuwar sa kan cewa ko bayan Tinubu ya bar mulki, “zai yi wahala a warware abubuwan da ya kafa tare da kuma magance waɗannan matsalolin.”

Atiku ya yi zargin cewa Tinubu na saƙala harkokin kasuwancinsa cikin harkokin gwamnati a Legas, tare da cewar irin hakan ne ke faruwa a yanzu a matakin tarayya.

Atiku ya ce a sanarwar “na yi matuƙar mamaki da gano cewa kamfanin man fetur na Najeriya (NNPCL) ya sanya ayyukansa na sayar da kayayyaki a ƙarƙashin kulawar OVH, wani kamfanin da Oando ke MALLAKIN kashi 49 cikin ɗari.”

“Oando fa yana ƙarkashin jagorancin Wale Tinubu ne, ƙanen Shugaban Tinubu.” in ji sanarwar.

Atiku ya bayyana baƙin cikinsa kan yadda a cewarsa “wasu kamfanoni da ke da kusanci da Tinubu suka dabaibaye harkokin kamfanin NNPCL ba bisa ka’ida ba.”

A wani sakon da ya wallafa a shafin sa na X a ranar Litinin, Atiku ya soki gwamnatin Tinubu kan cire tallafin man fetur wanda shi ne tushen halin da ƴan Najeriya ke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp