Home Labarai Tinubu na neman mallaka wa kansa Nijeriya – Atiku

Tinubu na neman mallaka wa kansa Nijeriya – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, ya zargi shugaban ƙasar, Bola Tinubu da ‘neman mayar da Najeriya mallakin kansa’.

Atiku, ɗan takarar jam’iyyar PDP a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023 ya yi iƙirarin cewa Tinubu yana jinginar da makoman matasan Nijeriya ga kansa da iyalinsa da kuma abokansa na kusa.

Atiku ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe ya fitar a ranar Laraba, inda ya bayyana damuwar sa kan cewa ko bayan Tinubu ya bar mulki, “zai yi wahala a warware abubuwan da ya kafa tare da kuma magance waɗannan matsalolin.”

Atiku ya yi zargin cewa Tinubu na saƙala harkokin kasuwancinsa cikin harkokin gwamnati a Legas, tare da cewar irin hakan ne ke faruwa a yanzu a matakin tarayya.

Atiku ya ce a sanarwar “na yi matuƙar mamaki da gano cewa kamfanin man fetur na Najeriya (NNPCL) ya sanya ayyukansa na sayar da kayayyaki a ƙarƙashin kulawar OVH, wani kamfanin da Oando ke MALLAKIN kashi 49 cikin ɗari.”

“Oando fa yana ƙarkashin jagorancin Wale Tinubu ne, ƙanen Shugaban Tinubu.” in ji sanarwar.

Atiku ya bayyana baƙin cikinsa kan yadda a cewarsa “wasu kamfanoni da ke da kusanci da Tinubu suka dabaibaye harkokin kamfanin NNPCL ba bisa ka’ida ba.”

A wani sakon da ya wallafa a shafin sa na X a ranar Litinin, Atiku ya soki gwamnatin Tinubu kan cire tallafin man fetur wanda shi ne tushen halin da ƴan Najeriya ke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp