Home General Gwamnan Jihar Sokoto ya magantu kan kisan sarkin Gobir

Gwamnan Jihar Sokoto ya magantu kan kisan sarkin Gobir

Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu ya miƙa ta’aziyarsa a kan rasuwar Hakimin Gatawa Alhaji Isa Muhammed Bawa, wanda ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane.

A saƙon jajen, gwamnan ya ce yana miƙa saƙon jajensa zuwa ga iyalan marigayin da mutanen Sabon Birni da dukkan mutanen jihar.

Cikin wata sanarwa da Sakataren Watsa Labaransa, Abubakar Bawa ya fitar, Aliyu ya ce gwamnatinsa ba za ta huta ba har sai an kawo ƙarshen ayyukan ƴan bindiga a jihar.

Gwamna Aliyu ya bayyana kisan a matsayin “rashin tausayi da dabbanci”, wanda dole a yi Allah-wadai da shi.

Sanarwar ta bayyana mamacin a matsayin mai gaskiya da amana, da son zaman lafiya wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen aiki ga al’umma.

Dokta Aliyu ya yi kira ga jami’an tsaro a jihar da su ƙara ƙoƙari a kan wanda suke yi domin tabbatar da tsaro a jihar, sannan su yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da cewa an kama waɗanda suka kashe hakimin domin su fuskanci hukunci.

Tuni dai Al’ummar garin Sabon Birni a jihar suka gudanar da sallar janazar Sarkin Gobir na Gatawa, Isa Bawa da safiyar yau Alhamis, bayan kashe shi da ƴan bindiga suka yi.

Labarin kisan sarkin ya ɓulla ne a ranar Laraba, bayan da bayanai suka tabbatar da cewa ƴan bindigar sun halaka shi duk da neman kuɗin fansa da suka yi.

Ɗaruruwan mutane ne suka hallara domin gudanar da sallar a garin Sabon Birni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp