Home General Ambaliyar ruwa ta raba dubbai da muhallinsu a jihar Sokoto – NEMA

Ambaliyar ruwa ta raba dubbai da muhallinsu a jihar Sokoto – NEMA

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta ce ambaliyar ruwa ta raba dubban mutane da muhallansu a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin ƙasar.

wannan na cikin wata sanarwa da hukumar ta NEMA ta wallafa a shafinta na X, in da ta ce ambaliyar da ta faru ranar Litinin ta shafi garuruwa kusan 20 a ƙananan hukumomin Shagari da Tureta.

“Ruwan ya shafe gadar da ke haɗa Shagari da Tureta baki ɗaya kuma ya hana mutane zirga-zirga a yankin,” a cewar sanarwar.

“Haka nan ambaliyar ta shafi ayyukan noma, inda ta shafe gonaki da dama.”

ko dai a ‘yan tsakanin nan Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet), ta yi gargaɗin samun ambaliyar a wasu jihohin ƙasar sakamakon mamakon ruwan sama da za a samu kwanan nan.

Hukumar ta ce jihohin da suka haɗa da Kano, da Katsina, da Zamfara, da Jigawa da Kebbi da Kaduna, da kuma jihar Adamawa na cikin barazanar fuskantar ambaliyar ruwa.

ko da yake dai hukumar bata ambaci jihar Sokoto a cikin jerin jihohin da zasu iya samun ambaliyar ba, ko da yake ta bukaci suaran al’umma dasu dauki matakin da suka dace wajen gyara magunan ruwan su tare da kaucewa yin gini akan hanyar ruwa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp