Home General Ambaliyar ruwa ta raba dubbai da muhallinsu a jihar Sokoto – NEMA

Ambaliyar ruwa ta raba dubbai da muhallinsu a jihar Sokoto – NEMA

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta ce ambaliyar ruwa ta raba dubban mutane da muhallansu a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin ƙasar.

wannan na cikin wata sanarwa da hukumar ta NEMA ta wallafa a shafinta na X, in da ta ce ambaliyar da ta faru ranar Litinin ta shafi garuruwa kusan 20 a ƙananan hukumomin Shagari da Tureta.

“Ruwan ya shafe gadar da ke haɗa Shagari da Tureta baki ɗaya kuma ya hana mutane zirga-zirga a yankin,” a cewar sanarwar.

“Haka nan ambaliyar ta shafi ayyukan noma, inda ta shafe gonaki da dama.”

ko dai a ‘yan tsakanin nan Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet), ta yi gargaɗin samun ambaliyar a wasu jihohin ƙasar sakamakon mamakon ruwan sama da za a samu kwanan nan.

Hukumar ta ce jihohin da suka haɗa da Kano, da Katsina, da Zamfara, da Jigawa da Kebbi da Kaduna, da kuma jihar Adamawa na cikin barazanar fuskantar ambaliyar ruwa.

ko da yake dai hukumar bata ambaci jihar Sokoto a cikin jerin jihohin da zasu iya samun ambaliyar ba, ko da yake ta bukaci suaran al’umma dasu dauki matakin da suka dace wajen gyara magunan ruwan su tare da kaucewa yin gini akan hanyar ruwa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp