Home General Ambaliyar ruwa ta raba dubbai da muhallinsu a jihar Sokoto – NEMA

Ambaliyar ruwa ta raba dubbai da muhallinsu a jihar Sokoto – NEMA

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta ce ambaliyar ruwa ta raba dubban mutane da muhallansu a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin ƙasar.

wannan na cikin wata sanarwa da hukumar ta NEMA ta wallafa a shafinta na X, in da ta ce ambaliyar da ta faru ranar Litinin ta shafi garuruwa kusan 20 a ƙananan hukumomin Shagari da Tureta.

“Ruwan ya shafe gadar da ke haɗa Shagari da Tureta baki ɗaya kuma ya hana mutane zirga-zirga a yankin,” a cewar sanarwar.

“Haka nan ambaliyar ta shafi ayyukan noma, inda ta shafe gonaki da dama.”

ko dai a ‘yan tsakanin nan Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet), ta yi gargaɗin samun ambaliyar a wasu jihohin ƙasar sakamakon mamakon ruwan sama da za a samu kwanan nan.

Hukumar ta ce jihohin da suka haɗa da Kano, da Katsina, da Zamfara, da Jigawa da Kebbi da Kaduna, da kuma jihar Adamawa na cikin barazanar fuskantar ambaliyar ruwa.

ko da yake dai hukumar bata ambaci jihar Sokoto a cikin jerin jihohin da zasu iya samun ambaliyar ba, ko da yake ta bukaci suaran al’umma dasu dauki matakin da suka dace wajen gyara magunan ruwan su tare da kaucewa yin gini akan hanyar ruwa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp