Home Labarai ‘Yan sanda sun kama bata gari 41 a jihar Kano

‘Yan sanda sun kama bata gari 41 a jihar Kano

Rundunar Yan Sandan jihar Kano, ta kama mutane 41 da ake Zargi da addabar jama’a, sassan jihar.

Wannan ya biyo bayan rahotannin da Rundunar Yan Sandan ta samu kan yadda batagarin suke zama tare da addabar mutane.

Mai magana da yawun Rundunar Yan Sandan jahar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa kwamishinan yan Sandan jahar CP Salman Dogo Garba, ya bayar umarnin shiga wuraren tare kama mutane 41 da kuma makamai da kayan maye da aka samu a wajensu.

Kwamishinan yan Sandan ya godewa al’ummar jahar Kano, bisa hadin kan da suke bayarwa domin duk irin wani laifi da ake aikata wa a jahar Yana raguwa.

Kiyawa, ya kara da cewa daman tuni babban sufeton Yan Sandan Nijeriya Kayode Adeolu Egbetokun, ya bayar da umarnin Fadada Sintiri da kuma tabbatar da amfani da bayanan sirri domin inganta tsaro.

Rundunar Yan Sandan jihar Kano karkashin jagorancin CP Salman Dogo Garba, ta yi babbar nasarar magance matsaloli na tsaro, Inda aka gudanar da Sintiri a lungu da sako na kwaryar birnin Kano, tare da Kai sumame a wuraren da ake Zargin batagarin matasa suna aika-aika a wuraren.

Sumamen ya Kai ga cafke mutane 41 da makamai da kuma kayan mayen da suke sha suna buguwa.

Wannan ya biyo bayan dagewar da Rundunar Yan Sandan ta yi, domin ganin an tabbatar da tsaro a Kano gaba daya.

Haka zalika Rundunar Yan Sandan ta kara godewa al’umma , saboda an samu raguwar aikata laifuka a wannan lokaci da ake ciki.

CP Dogo Garba, ya tabbatar wa da al’umma cewa za su ci gaba da zage damtse na tabbatar da tsaro da kare rayuka, lafiya da kuma dukiyoyon su.

A karshe Rundunar ta Yi kiran a ci gaba da ba wa Rundunar Yan Sandan jahar Kano, hadin Kai domin ci gaba da tabbatar da tsaro da zaman lafiya, Inda rundunar ta bayar da nambobin Waya don sanar da ita wani motsi ko wani Abu da ba a amince da shi ba ko agajin gaggawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp