Home Labarai ‘Yan sanda sun kama bata gari 41 a jihar Kano

‘Yan sanda sun kama bata gari 41 a jihar Kano

Rundunar Yan Sandan jihar Kano, ta kama mutane 41 da ake Zargi da addabar jama’a, sassan jihar.

Wannan ya biyo bayan rahotannin da Rundunar Yan Sandan ta samu kan yadda batagarin suke zama tare da addabar mutane.

Mai magana da yawun Rundunar Yan Sandan jahar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa kwamishinan yan Sandan jahar CP Salman Dogo Garba, ya bayar umarnin shiga wuraren tare kama mutane 41 da kuma makamai da kayan maye da aka samu a wajensu.

Kwamishinan yan Sandan ya godewa al’ummar jahar Kano, bisa hadin kan da suke bayarwa domin duk irin wani laifi da ake aikata wa a jahar Yana raguwa.

Kiyawa, ya kara da cewa daman tuni babban sufeton Yan Sandan Nijeriya Kayode Adeolu Egbetokun, ya bayar da umarnin Fadada Sintiri da kuma tabbatar da amfani da bayanan sirri domin inganta tsaro.

Rundunar Yan Sandan jihar Kano karkashin jagorancin CP Salman Dogo Garba, ta yi babbar nasarar magance matsaloli na tsaro, Inda aka gudanar da Sintiri a lungu da sako na kwaryar birnin Kano, tare da Kai sumame a wuraren da ake Zargin batagarin matasa suna aika-aika a wuraren.

Sumamen ya Kai ga cafke mutane 41 da makamai da kuma kayan mayen da suke sha suna buguwa.

Wannan ya biyo bayan dagewar da Rundunar Yan Sandan ta yi, domin ganin an tabbatar da tsaro a Kano gaba daya.

Haka zalika Rundunar Yan Sandan ta kara godewa al’umma , saboda an samu raguwar aikata laifuka a wannan lokaci da ake ciki.

CP Dogo Garba, ya tabbatar wa da al’umma cewa za su ci gaba da zage damtse na tabbatar da tsaro da kare rayuka, lafiya da kuma dukiyoyon su.

A karshe Rundunar ta Yi kiran a ci gaba da ba wa Rundunar Yan Sandan jahar Kano, hadin Kai domin ci gaba da tabbatar da tsaro da zaman lafiya, Inda rundunar ta bayar da nambobin Waya don sanar da ita wani motsi ko wani Abu da ba a amince da shi ba ko agajin gaggawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp