Home Labarai ‘Yan sanda sun kama bata gari 41 a jihar Kano

‘Yan sanda sun kama bata gari 41 a jihar Kano

Rundunar Yan Sandan jihar Kano, ta kama mutane 41 da ake Zargi da addabar jama’a, sassan jihar.

Wannan ya biyo bayan rahotannin da Rundunar Yan Sandan ta samu kan yadda batagarin suke zama tare da addabar mutane.

Mai magana da yawun Rundunar Yan Sandan jahar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa kwamishinan yan Sandan jahar CP Salman Dogo Garba, ya bayar umarnin shiga wuraren tare kama mutane 41 da kuma makamai da kayan maye da aka samu a wajensu.

Kwamishinan yan Sandan ya godewa al’ummar jahar Kano, bisa hadin kan da suke bayarwa domin duk irin wani laifi da ake aikata wa a jahar Yana raguwa.

Kiyawa, ya kara da cewa daman tuni babban sufeton Yan Sandan Nijeriya Kayode Adeolu Egbetokun, ya bayar da umarnin Fadada Sintiri da kuma tabbatar da amfani da bayanan sirri domin inganta tsaro.

Rundunar Yan Sandan jihar Kano karkashin jagorancin CP Salman Dogo Garba, ta yi babbar nasarar magance matsaloli na tsaro, Inda aka gudanar da Sintiri a lungu da sako na kwaryar birnin Kano, tare da Kai sumame a wuraren da ake Zargin batagarin matasa suna aika-aika a wuraren.

Sumamen ya Kai ga cafke mutane 41 da makamai da kuma kayan mayen da suke sha suna buguwa.

Wannan ya biyo bayan dagewar da Rundunar Yan Sandan ta yi, domin ganin an tabbatar da tsaro a Kano gaba daya.

Haka zalika Rundunar Yan Sandan ta kara godewa al’umma , saboda an samu raguwar aikata laifuka a wannan lokaci da ake ciki.

CP Dogo Garba, ya tabbatar wa da al’umma cewa za su ci gaba da zage damtse na tabbatar da tsaro da kare rayuka, lafiya da kuma dukiyoyon su.

A karshe Rundunar ta Yi kiran a ci gaba da ba wa Rundunar Yan Sandan jahar Kano, hadin Kai domin ci gaba da tabbatar da tsaro da zaman lafiya, Inda rundunar ta bayar da nambobin Waya don sanar da ita wani motsi ko wani Abu da ba a amince da shi ba ko agajin gaggawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp