Home General Sojojin saman Nijeriya sun hallaka kwamandojin boko haram a Borno

Sojojin saman Nijeriya sun hallaka kwamandojin boko haram a Borno

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce sojojinta masu aiki ƙarƙashin shirin ‘Operation Hadin Kai’ da ke yaƙi da ayyukan masu tayar da ƙayar baya sun kashe manyan kwamandojin Boko Haram a hare-hare ta sama da suka kai a a ranar 16 ga wannan wata na Agusta a jihar Borno.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar da rundunar ta fitar ta hannun mai magana da yawunta AVM Edward Gabkwet a yau Laraba.

Sanarwar ta ce “rundunar ta kai harin ne kan ƴan ta’addan da suka yi hijira zuwa yankin daga wasu wurare da ke kusa”.

“Hare-haren sojojin ta sama sun yi nasarar halaka ƴan ta’adda da dama da suka hada da manyan kwamandojinsu biyar da kuma yaransu 35 tare da lalata maɓoyarsu da kayan aikinsu.

“Bayanai masu ƙarfi da aka tattara sun nuna cewa manyan ƴan ta’adda da ke a wurin da aka kai harin a daidai lokacin sun haɗa da Munzir Arika, Sani Dilla (Dan Hausawan Jubillaram), Ameer Modu, Dan Fulani Fari Fari, da Bakoura Arina Chiki, sai kuma sauran wasu ƴan bindiga 35.”

Sanarwar ta ce “Ana sa ran nasarar kashe waɗannan kwamandojin da mayakansu zai rage ƙarfin wadannan kungiyoyi ƴan ta’adda na ƙara kai hare-hare ko sake haɗuwa a yankin.”

Najeriya na yaƙi da mayaƙan ƙungiyar Boko Haram tsawon sama da shekaru 10 da suka gabata, rikicin da ya yi sanadin mutuwar dubban al’umma da kuma tarwatsa sama da mutum miliyan ɗaya daga gidajensu.

Duk da cewa gwamnatin Najeriya ta yi iƙirarin karya lagon mayaƙan, amma har yanzu akan samu hare-hare nan da can a yankin na arewa maso gabashin ƙasar.

A ƙarshen watan Yuli, wasu mayaƙa da ake zargin ƴan Boko Haram ne sun kai hari a jihar ta Borno wanda ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 16.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp