Home General Sojojin saman Nijeriya sun hallaka kwamandojin boko haram a Borno

Sojojin saman Nijeriya sun hallaka kwamandojin boko haram a Borno

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce sojojinta masu aiki ƙarƙashin shirin ‘Operation Hadin Kai’ da ke yaƙi da ayyukan masu tayar da ƙayar baya sun kashe manyan kwamandojin Boko Haram a hare-hare ta sama da suka kai a a ranar 16 ga wannan wata na Agusta a jihar Borno.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar da rundunar ta fitar ta hannun mai magana da yawunta AVM Edward Gabkwet a yau Laraba.

Sanarwar ta ce “rundunar ta kai harin ne kan ƴan ta’addan da suka yi hijira zuwa yankin daga wasu wurare da ke kusa”.

“Hare-haren sojojin ta sama sun yi nasarar halaka ƴan ta’adda da dama da suka hada da manyan kwamandojinsu biyar da kuma yaransu 35 tare da lalata maɓoyarsu da kayan aikinsu.

“Bayanai masu ƙarfi da aka tattara sun nuna cewa manyan ƴan ta’adda da ke a wurin da aka kai harin a daidai lokacin sun haɗa da Munzir Arika, Sani Dilla (Dan Hausawan Jubillaram), Ameer Modu, Dan Fulani Fari Fari, da Bakoura Arina Chiki, sai kuma sauran wasu ƴan bindiga 35.”

Sanarwar ta ce “Ana sa ran nasarar kashe waɗannan kwamandojin da mayakansu zai rage ƙarfin wadannan kungiyoyi ƴan ta’adda na ƙara kai hare-hare ko sake haɗuwa a yankin.”

Najeriya na yaƙi da mayaƙan ƙungiyar Boko Haram tsawon sama da shekaru 10 da suka gabata, rikicin da ya yi sanadin mutuwar dubban al’umma da kuma tarwatsa sama da mutum miliyan ɗaya daga gidajensu.

Duk da cewa gwamnatin Najeriya ta yi iƙirarin karya lagon mayaƙan, amma har yanzu akan samu hare-hare nan da can a yankin na arewa maso gabashin ƙasar.

A ƙarshen watan Yuli, wasu mayaƙa da ake zargin ƴan Boko Haram ne sun kai hari a jihar ta Borno wanda ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 16.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp