Home General Abin da ya sa ban amsa gayyatar ‘yan sanda ba – Joe...

Abin da ya sa ban amsa gayyatar ‘yan sanda ba – Joe Ajaero

Shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya NLC, Joe Ajaero, ya bayyana cewa zai mutunta gayyatar da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta yi masa a ranar Laraba 29 ga watan Agustan 2024, maimakon yau Talata 20 ga watan Agustan 2024 kamar yadda aka buƙata tun farko.

A cikin wata wasiƙa da shugaban ƙwadagon ya aika wa ƴansanda ta hannun lauyoyinsa, Ajaero ya bayyana cewa, wasikar gayyatar ta same shi ne a jiya Litinin, kuma shugaban yana da wasu ayyukan da ya tsara gudanarwa a yau Talata.

Sai dai sanarwar ta ce Ajaero a shirye yake ya amsa gayyatar a ranar Laraba.

Bugu da kari, Ajaero ya buƙaci ƴansanda da su bayar da cikakkun bayanai game da zargin da ake yi masa, waɗanda suka haɗa da samar da kuɗaɗen tallafa wa ayyukan ta’addanci da haɗa baki wajen aikata laifuffuka da cin amanar ƙasa, da kuma aikata laifuka ta shafukan intanet.

Wasiƙar ta ambato sashe na 36 na kundin tsarin mulkin Najeriya, wanda ya bai wa wanda ake tuhuma ƴancin samun cikakken bayani game da yanayi da takamaiman zarge-zargen da ake yi masa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp