Home Labarai NLC ta yi barazanar tsayar da Nijeriya Cak

NLC ta yi barazanar tsayar da Nijeriya Cak

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya NLC, ta yi gargaɗi tare da yin barazanar fara yajin aikin sai baba-ta-gani, idan har aka kama shugabanta, Joe Ajaero.

Ƙungiyar ta yanke wannan shawarar ne a wani taron gaggawa da jagororinta suka gudanar a yau, Talata.

Taron ya gudana ne bayan gayyatar da rundunar ƴansandan Najeriya ta yi wa shugaban ƙungiyar, Joe Ajaero, wanda ta ce hakan na da alaƙa ne da bincikensa da ake yi kan zargin samar da kuɗade domin tallafa wa ayyukan ta’addanci, da aikata laifuffuka ta shafukan intanet, da zamba, da haɗa baki wajen aikata laifuka da kuma cin amanar ƙasa.

Sai dai a nata ɓangaren, NLC ta bayyana zarge-zargen a matsayin marasa tushe kuma ta yi zargin cewa lamarin na da alaƙa da siyasa.

Ƙungiyar ƙwadagon ta zargi mahukuntan Najeriya da yunƙurin tursasawa da kuma musguna wa shugabanninta.

Ta kuma ce ana ƙoƙari ne wajen ganin an raunana ta bisa ‘fafutikar da take ta kare manufofin dimokuradiyya da haƙƙokin ma’aikatan Najeriya’.

Saboda haka ne jagororin ƙungiyar suka umarci dukkanin ɓangarorin ƙungiyar su fara haɗa kan mambobinsu a faɗin ƙasar da gargaɗin cewa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ɗaukar dukkan matakan da suka dace, waɗanda suka haɗa da zanga-zanga da kuma dakatar da komai a ƙasar don kare mutunci da ƴancin kai na ƙungiyar.

“Idan har wani abu ya faru da shugabanmu, ko kuma aka kama shi, to za mu fara yajin aikin sai baba ta gani a faɗin ƙasar daga tsakar dare.” in ji NLC.

NLC na ɗaya daga cikin ƙungiyoyin ƙwadago mafiya ƙarfin faɗa a ji a Najeriya, wadda a lokuta da dama ta jagoranci ma’aikata domin nuna rashin amincewa da wasu manufofin gwamnati.

Ko a wannan shekara ta 2024, ƙungiyar ta shiga yajin aiki tare da gudanar da zanga-zanga bayan zargin gwamnati da rashin mayar da hankali a batun ƙarin albashin ma’aikata.

Hakan ya tursasa wa gwamnatin ƙasar sake kiran ƙungiyar zuwa teburin shawarwari, inda daga ƙarshe aka cimma matsayar nunka albashin ma’aikata daga naira 30,000 zuwa naira 70,000.

Sai dai daga baya an ga alamu na rashin jituwa tsakanin ɓangarorin biyu bayan da ƙungiyar ta NLC ta ce ba za ta janye daga zanga-zangar matsin rayuwa da aka gudanar a ƙasar ba kasancewar ba ita ce ta shirya ta ba.

Jim kaɗan bayan hakan ne wasu jami’an tsaro suka kai samame a babban ofishin ƙungiyar da ke Abuja, sai dai bayan koken da ƙungiyar ta yi, rundunar ƴansandan Najeriya ta ce ta kai samamen ne domin gano wasu muhimman takardu waɗanda za su zamo shaida a binciken da ake yi kan wani mutum, wanda ‘ke da hatsari’ ga ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp