Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinubu ya ce yayi matukar kaduwa da jin yadda yan bindiga suka kashe sarkin Gobir,tare da cin alwashin daukar mataki akan masu garkuwa.
A cikin sanarwar da mai Magana da yawun shugaban Najeriya Ajuri Ngelele ya fitar, ya ce shugaban ya bayyana kisan basaraken a matsayin cin zarafi da kuma tozarci da bazai bari a cigaba da aikawa ba.
Read Also:
Ya kumayi ta’aziyya ga iyalan marigayin, da masarautar Gobir da ma gwamnatin Sokoto.
Ya kuma yiwa ‘yan Najeriya albishir da cewar gwamnatinsa a shirye take wajan yakin ayyukan ‘yan ta’addah.
shugaban ya bayyana cewar yana yin duk mai yuwuwa wajan ganin ya tabbatar da tsaro a kasar, sai ‘yan siyasa da al’ummar kasar na cigaba da bayyana takaicin su gane da rashin tsaro da yafi kamari a yankin arewacin kasar.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1464 days 16 hours 49 minutes 46 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1446 days 18 hours 31 minutes 11 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com