Home General Tinubu ya ƙara wa babban sufeton ‘yan sandan Najeriya wa’adin shekaru 3

Tinubu ya ƙara wa babban sufeton ‘yan sandan Najeriya wa’adin shekaru 3

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙarawa Babban Sefotun ‘yan sandan kasar Kayode Egbetokun wa’adi, kamar yadda wata majiya daga ofishin sakataren gwamnatin tarayya ta bayyana.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito an ƙara wa shugaban ‘yan sandan wa’adin shekara uku ne, ma’ana sai zuwa 2027.

Ta ruwaito cewa Sakataren Gwamnatin Tarayya George Akume ne ya bai wa Babban Sufeton ‘yan sandan takartar ƙara masa wa’adin a ranar Litinin.

A watan Yulin da ya gabata ne Majalisar Dattijan Najeriya ta yi garambawul ga dokar ‘yan sanda ta 2020 ƙarƙashin sashe na 8, wadda ta ci karo da ƙarawa ma’aikacin gwamnati wa’adin aiki bayan shekara 35 ko kuma bayan kaiwa shekara 60 a raye.

Egbetokun wanda aka naɗa IG a watan Yunin 2023 zai cika shekara 60 ne a gobe 4 ga watan Satumba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp