Home General Sojojin Saman Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 5 a jihar Kaduna

Sojojin Saman Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 5 a jihar Kaduna

Dakarun sojojin saman Nijeriya sun sami nasarar halaka jagoran ‘Yan ta’addan da ya addabi al’umma a jihar Kaduna Mustapha Abdullahi, da wasu yaran sa biyar a karamar hukumar Igabi dake jihar.

Daraktan yada labaran rundunar sojin AVM Edward Gabkwet ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar ranar lahadi, in da ya ce dakarun da rundunar sojin ta 413 ne suka sami nasarar kan gungun ‘yan ta’addan.

Sanarwar ta ce yayi da suke aiki da bayanan sirrin da suka samu dakarun na musamman da aka girke a dajin Sabon Gida, a kokarin da suke na kakkabe ayyukan ‘yan Ta’addan dake addabar Al’umma suka sami damar tarwatsa gungun ‘yan bindigar.

A yayin atisayen sojojin sun sami nasarar kwato makamai masu tarin yawa da suka hadar da bindiga kirar gida guda biyar, da wata babbar binidga kirar gida guda daya, sai kuma alburusai masu tarin yawa da sauran makamai.

Gabkwet yace ‘yan ta’addan nada aniyar aikata garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, cutarwa gami da hallaka fararen hula da basu ji ba basu gani ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp