Home General Sojojin Saman Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 5 a jihar Kaduna

Sojojin Saman Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 5 a jihar Kaduna

Dakarun sojojin saman Nijeriya sun sami nasarar halaka jagoran ‘Yan ta’addan da ya addabi al’umma a jihar Kaduna Mustapha Abdullahi, da wasu yaran sa biyar a karamar hukumar Igabi dake jihar.

Daraktan yada labaran rundunar sojin AVM Edward Gabkwet ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar ranar lahadi, in da ya ce dakarun da rundunar sojin ta 413 ne suka sami nasarar kan gungun ‘yan ta’addan.

Sanarwar ta ce yayi da suke aiki da bayanan sirrin da suka samu dakarun na musamman da aka girke a dajin Sabon Gida, a kokarin da suke na kakkabe ayyukan ‘yan Ta’addan dake addabar Al’umma suka sami damar tarwatsa gungun ‘yan bindigar.

A yayin atisayen sojojin sun sami nasarar kwato makamai masu tarin yawa da suka hadar da bindiga kirar gida guda biyar, da wata babbar binidga kirar gida guda daya, sai kuma alburusai masu tarin yawa da sauran makamai.

Gabkwet yace ‘yan ta’addan nada aniyar aikata garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, cutarwa gami da hallaka fararen hula da basu ji ba basu gani ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp