Home General Sojojin Saman Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 5 a jihar Kaduna

Sojojin Saman Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 5 a jihar Kaduna

Dakarun sojojin saman Nijeriya sun sami nasarar halaka jagoran ‘Yan ta’addan da ya addabi al’umma a jihar Kaduna Mustapha Abdullahi, da wasu yaran sa biyar a karamar hukumar Igabi dake jihar.

Daraktan yada labaran rundunar sojin AVM Edward Gabkwet ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar ranar lahadi, in da ya ce dakarun da rundunar sojin ta 413 ne suka sami nasarar kan gungun ‘yan ta’addan.

Sanarwar ta ce yayi da suke aiki da bayanan sirrin da suka samu dakarun na musamman da aka girke a dajin Sabon Gida, a kokarin da suke na kakkabe ayyukan ‘yan Ta’addan dake addabar Al’umma suka sami damar tarwatsa gungun ‘yan bindigar.

A yayin atisayen sojojin sun sami nasarar kwato makamai masu tarin yawa da suka hadar da bindiga kirar gida guda biyar, da wata babbar binidga kirar gida guda daya, sai kuma alburusai masu tarin yawa da sauran makamai.

Gabkwet yace ‘yan ta’addan nada aniyar aikata garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, cutarwa gami da hallaka fararen hula da basu ji ba basu gani ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp