Home General Annobar amai da gudawa ta hallaka mutane bakwai a jihar Jigawa

Annobar amai da gudawa ta hallaka mutane bakwai a jihar Jigawa

Gwamnatin jihar Jigawa dake arewa Maso yammacin kasar ta tabbata da barkewar annobar amai da gudawa a karamar hukumar kirikasamma, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane bakwai tare da kwantar da dama a Asibitin jihar.

Shugaban kula da lafiyar al’umma na yankin na kirikasamma, Musa Abdullahi Diladige ne, ya tabbatar da barkewar cutar a yankunan Malori, Maikintari, Dilmari, Kirikasamma, da wani bangare na kauyen Baturiya.

Diladige, ya bayyana cewa wadanda abin ya shafa na fama da alamomin rashin lafiya masu tsanani kamar gudawa, kumburin ciki, amai, da zazzabi

An tura ma’aikatan lafiya zuwa yankunan don samar da agajin gaggawa.

Hukumomi sun dauki matakin gaggawa ta hanyar sayan magungunan da ake bukata don fara jinyar masu cutar.

Daraktan gudanarwa da ayyukan gama-gari, Idris Gambo Abubakar, ya yi alkawarin bayar da goyon bayan da ake bukata don dakile yaduwar cutar.

Ana kyautata zaton ruwan sama mai tsanani da aka samu a yankin ne ya haifar da barkewar cutar, inda gine-gine suka lalace kuma hanyoyin samar da ruwa suka lalace.

An shawarci mazauna yankin da su dauki matakan kariya nan take.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp