Home General Hukumar gidajen yarin Kano ta musanta zargin rashin bai wa fursunoni wadataccen...

Hukumar gidajen yarin Kano ta musanta zargin rashin bai wa fursunoni wadataccen abinci

Hukumar Kula da Gidajen Yarin Najeriya reshen jihar Kano ta musanta rahotonnin da wasu kafofin yaɗa labaran ƙasar suka ruwaito na rashin bai wa fursunonin da ke ɗaure a gidajen yarin jihar wadataccen abinci.

A baya-baya nan dai an yi ta samun labaran ƙorafe-ƙorafe kan rashin bai wa fursunonin wadataccen abinci a jihar a shafukan sada zumunta.

To sai dai cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar kula da gidajen yarin jihar, Musbahu Lawan K/Nasarawa ya fitar ya ce an yaɗa rahotonni ne kawai domin ɓata wa hukumarsu suna.

”Waɗannan rahotonni abin takaici ne, kuma hukumarmu na shaida wa al’umma cewa walwala da jin daɗin fusunoninmu shi ne babban abin da hukumarmu ta sanya a gaba, don haka ne koyaushe hukumarmu ke tabbatar wannan muradi duk kuwa da halin matsin tattalin arziki da ƙarsamu ke ciki”, in ji sanarwar.

Ya kuma ƙara da cewa ba abinci kawai hukumar hukumar ke bai wa fursunonin ba, har ma da ilimantar da su da kuma ba su horon sana’o’in dogaro da kai da za su taimaki rayuwarsu bayan kammala zaman gidan yarin.

A Najeriya ana yawan samun ƙorafe-ƙorafe kan halin da ɗaurarru ke ciki a gidajen yarin ƙasar, kama daga kula da lafiyarsu da abinci da kuma babbar matsalar cunkoson fursunoni a gidajen yarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp