Majalisar wakilan Nijeriya ta magantu kan karin farashin Man Fetur

Gamayyar marasa rinjaye a Majalisar Wakilan Nijeriya ta nemi a gaggauta janye ƙarin farashin man fetur da aka ƙara kwanan nan, saboda hakan zai ƙara wa ‘yan Najeriya wahala.

Sanarwar da shugabansu Kingsley Chinda ya fitar ta ce an kara wannan farashin ne ba tare da tuntubar masu ruwa da tsaki ba, ya saba wa ka’idojin gaskiya, da adalci da ya kamata su zama jagora a yanke irin wannan shawara mai tasiri ga rayuwar jama’a.

Sanarwar ta ƙara da cewa ƙarin farashin Man zai haifar da ƙarin matsalolin tattalin arziki da suka haɗa da tsadar sufuri, kayan abinci, da sauran muhimman kayayyaki, wanda zai ƙara jefa ƙarin iyalai cikin talauci.

Marasa rinjayen sun ce rashin tuntubar Majalisar Tarayya da sauran masu ruwa da tsaki game da wannan ƙarin ba daidai ba ne, yayin da suka gargadi gwamnati da ta yi tunani a kan halin da ƙasa ke ciki na rashin aikin yi, tsadar rayuwa, da rashin daidaito, domin wannan na iya haifar da tarzoma da ƙarin fitina a cikin ƙasa.

A ƙarshe, sun yi kira ga gwamnatin Tinubu da ta gaggauta yin gyara tare da neman hanyoyin da za su kawo sauyi a tattalin arzikin ƙasar ba tare da ƙara wa jama’a wahala ba.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1187 days 17 hours 57 minutes 26 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1169 days 19 hours 38 minutes 51 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com