Home General Majalisar wakilan Nijeriya ta magantu kan karin farashin Man Fetur

Majalisar wakilan Nijeriya ta magantu kan karin farashin Man Fetur

Gamayyar marasa rinjaye a Majalisar Wakilan Nijeriya ta nemi a gaggauta janye ƙarin farashin man fetur da aka ƙara kwanan nan, saboda hakan zai ƙara wa ‘yan Najeriya wahala.

Sanarwar da shugabansu Kingsley Chinda ya fitar ta ce an kara wannan farashin ne ba tare da tuntubar masu ruwa da tsaki ba, ya saba wa ka’idojin gaskiya, da adalci da ya kamata su zama jagora a yanke irin wannan shawara mai tasiri ga rayuwar jama’a.

Sanarwar ta ƙara da cewa ƙarin farashin Man zai haifar da ƙarin matsalolin tattalin arziki da suka haɗa da tsadar sufuri, kayan abinci, da sauran muhimman kayayyaki, wanda zai ƙara jefa ƙarin iyalai cikin talauci.

Marasa rinjayen sun ce rashin tuntubar Majalisar Tarayya da sauran masu ruwa da tsaki game da wannan ƙarin ba daidai ba ne, yayin da suka gargadi gwamnati da ta yi tunani a kan halin da ƙasa ke ciki na rashin aikin yi, tsadar rayuwa, da rashin daidaito, domin wannan na iya haifar da tarzoma da ƙarin fitina a cikin ƙasa.

A ƙarshe, sun yi kira ga gwamnatin Tinubu da ta gaggauta yin gyara tare da neman hanyoyin da za su kawo sauyi a tattalin arzikin ƙasar ba tare da ƙara wa jama’a wahala ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp