Home General Gwamnatin Nijeriya tace zata kawo karshen wahalar Man Fetur a kasar

Gwamnatin Nijeriya tace zata kawo karshen wahalar Man Fetur a kasar

Ƙaramin Ministan Albarkatun Man Fetur, Heineken Lokpobiri ya ce daga yanzu zuwa ƙarshen mako man fetur zai wadata a ko’ina a faɗin ƙasar.

Ministan ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan ganawarsa da mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima a fadar shugaban ƙasar.

Ministan ya ce shugaban ƙasa ne ya buƙaci mataimakinsa ya kira taron na gaggawa domin sanin halin da ake ciki a game da batun man fetur.

A ranar Talata ne kamfanin NNPCL ya sanar da ƙarin farashin litar mai daga naira 617 zuwa naira 897.

“Abu mafi muhimmanci a yanzu shi ne akwai man, sannan muna da yaƙinin nan zuwa ƙarshen mako zai wadata a ko’ina a faɗin ƙasar nan.”

Ya ƙara da cewa farashin zai bambanta a wurare, “amma mun yi amannar cewa idan ya wadata, dole farashin zai ragu sosai.”

Ministan ta kuma bayyana cewa shugaban ƙasa ya damu da halin da ƴan Najeriya suke ciki, inda ya ce hakan ne ma ya sa ya umarci mataimakinsa ya kira taron domin tattaunawa da kuma neman mafita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp