Home General Gwamnatin Nijeriya tace zata kawo karshen wahalar Man Fetur a kasar

Gwamnatin Nijeriya tace zata kawo karshen wahalar Man Fetur a kasar

Ƙaramin Ministan Albarkatun Man Fetur, Heineken Lokpobiri ya ce daga yanzu zuwa ƙarshen mako man fetur zai wadata a ko’ina a faɗin ƙasar.

Ministan ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan ganawarsa da mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima a fadar shugaban ƙasar.

Ministan ya ce shugaban ƙasa ne ya buƙaci mataimakinsa ya kira taron na gaggawa domin sanin halin da ake ciki a game da batun man fetur.

A ranar Talata ne kamfanin NNPCL ya sanar da ƙarin farashin litar mai daga naira 617 zuwa naira 897.

“Abu mafi muhimmanci a yanzu shi ne akwai man, sannan muna da yaƙinin nan zuwa ƙarshen mako zai wadata a ko’ina a faɗin ƙasar nan.”

Ya ƙara da cewa farashin zai bambanta a wurare, “amma mun yi amannar cewa idan ya wadata, dole farashin zai ragu sosai.”

Ministan ta kuma bayyana cewa shugaban ƙasa ya damu da halin da ƴan Najeriya suke ciki, inda ya ce hakan ne ma ya sa ya umarci mataimakinsa ya kira taron domin tattaunawa da kuma neman mafita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp