Home General Gwamnatin Nijeriya tace zata kawo karshen wahalar Man Fetur a kasar

Gwamnatin Nijeriya tace zata kawo karshen wahalar Man Fetur a kasar

Ƙaramin Ministan Albarkatun Man Fetur, Heineken Lokpobiri ya ce daga yanzu zuwa ƙarshen mako man fetur zai wadata a ko’ina a faɗin ƙasar.

Ministan ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan ganawarsa da mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima a fadar shugaban ƙasar.

Ministan ya ce shugaban ƙasa ne ya buƙaci mataimakinsa ya kira taron na gaggawa domin sanin halin da ake ciki a game da batun man fetur.

A ranar Talata ne kamfanin NNPCL ya sanar da ƙarin farashin litar mai daga naira 617 zuwa naira 897.

“Abu mafi muhimmanci a yanzu shi ne akwai man, sannan muna da yaƙinin nan zuwa ƙarshen mako zai wadata a ko’ina a faɗin ƙasar nan.”

Ya ƙara da cewa farashin zai bambanta a wurare, “amma mun yi amannar cewa idan ya wadata, dole farashin zai ragu sosai.”

Ministan ta kuma bayyana cewa shugaban ƙasa ya damu da halin da ƴan Najeriya suke ciki, inda ya ce hakan ne ma ya sa ya umarci mataimakinsa ya kira taron domin tattaunawa da kuma neman mafita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp