Home General Majalisar wakilan Nijeriya ta magantu kan karin farashin Man Fetur

Majalisar wakilan Nijeriya ta magantu kan karin farashin Man Fetur

Gamayyar marasa rinjaye a Majalisar Wakilan Nijeriya ta nemi a gaggauta janye ƙarin farashin man fetur da aka ƙara kwanan nan, saboda hakan zai ƙara wa ‘yan Najeriya wahala.

Sanarwar da shugabansu Kingsley Chinda ya fitar ta ce an kara wannan farashin ne ba tare da tuntubar masu ruwa da tsaki ba, ya saba wa ka’idojin gaskiya, da adalci da ya kamata su zama jagora a yanke irin wannan shawara mai tasiri ga rayuwar jama’a.

Sanarwar ta ƙara da cewa ƙarin farashin Man zai haifar da ƙarin matsalolin tattalin arziki da suka haɗa da tsadar sufuri, kayan abinci, da sauran muhimman kayayyaki, wanda zai ƙara jefa ƙarin iyalai cikin talauci.

Marasa rinjayen sun ce rashin tuntubar Majalisar Tarayya da sauran masu ruwa da tsaki game da wannan ƙarin ba daidai ba ne, yayin da suka gargadi gwamnati da ta yi tunani a kan halin da ƙasa ke ciki na rashin aikin yi, tsadar rayuwa, da rashin daidaito, domin wannan na iya haifar da tarzoma da ƙarin fitina a cikin ƙasa.

A ƙarshe, sun yi kira ga gwamnatin Tinubu da ta gaggauta yin gyara tare da neman hanyoyin da za su kawo sauyi a tattalin arzikin ƙasar ba tare da ƙara wa jama’a wahala ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp