Kungiyar mata ‘yan jaridu reshen Kano NAWOJ ta ta bukaci daukacin al’ummar musulmi Nijeriya da su yi koyi da kyawawan halaye na fiyayyen halitta Annabi Muhammadu (S.A.W).
Wannan dai na cikin wata takardar manema labarai da kungiyar ta fitar, mai dauke da sa hannun sakatariyar kungiyar Maryam Muhammad a wani bangare na bikin murnar zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammadu S.A.W.
Read Also:
Sanarwar ta ambaci shugabar kungiyar Kwamared Bahijja Kabara na kira ga mata ‘yan jaridu da su rubanya kokarinsu ta hanyar bin koyarwar Annabi S A W wajen biyayya ga mazajensu da kuma kyautata alaka da makwabta.
Kwamaret Bahijja ta kuma yi kira ga mata da su koya wa ‘ya’yansu tarihin Annabi Muhammadu tare da yin koyi da halayensa domin kyautata rayuwar al’umma.
Hakazalika Kwamared Bahijja Kabara ya yi kira ga masu hannu da shuni da su taimaka wa marasa galihu kamar yadda aka koya daga koyarwar Annabi Muhd. S.A.W
PRNigeria Hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1463 days 20 minutes 45 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 2 hours 2 minutes 10 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com