Home General Gwamnatin Kano ta tallafawa wadanda gobara ta shafa a jihar Jigawa

Gwamnatin Kano ta tallafawa wadanda gobara ta shafa a jihar Jigawa

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya tallafawa mutanen da iftila’in fashewar tankar mai ya shafa a garin Majiya dake karamar hukumar Taura a jihar Jigawa da kyautar naira miliya 100.

Gwamnan ya bada tallafin ne lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya da jaje ga al’ummar jihar Jigawa bisa wannan ibtila’i wanda ya yi sanadiyyar rasa rayuka sama da 160 da kuma jikkata al’umma da dama.

Gwamna Abba ya miƙa ta’aziyyarsa a madadin gwamnati da al’ummar jihar Kano tare da fatan Allah ya kare afkuwar hakan a nan gaba.

Har ila yau gwamnan ya ƙara da cewa ibtila’in ba iya al’ummar jihar jigawa kaɗai ya shafa ba, har ma da al’umar jihar Kano, la’akari da dangantakar dake tsakanin jihohin biyu.

Daga nan ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suku rigamu gidan gaskiya ya bawa waɗanda suka jikkata lafiya.

A nasa bangaren, gwamnan jihar Jigawa Alhaji Umar Namadi Ɗanmoɗi ya godewa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa ziyarar jaje da ta’aziyyar da ya kaiwa al’ummar jihar, inda ya ce ziyarar zata kara karfafa dangantakar dake tsakanin jihohin biyu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp