Home Labarai Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta Kama Dan Sandan Bogi a jihar

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta Kama Dan Sandan Bogi a jihar

Rundunar  ‘yan sandna jihar kano ta sami nasarar kama wani matashi da take zargin da yin sojan gona, matsayin dan sandan bodi a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da Kakakin rundunar na kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar aka rabawa manema labarai a jihar a daren Alhamis, inda ya ce sun kama shi ne biyo bayan koken da al’umma suke yi a Kansa.

A cewar Kiyawa, “Mun kama wani matashin Salisu Bala mazaunin unguwar Kurna, a sakamakon yadda yake sojan gona da kakin ‘Yan Sanda yana karbar kudi a hannun al’umma da sunan shi Dan Sandan Sarauniya ne”.

Kuma dai yana gudanar da wannan aika-aikar tasa ne a unguwannin Sabon Gari, Fagge, Koki dake kwaryar birnin Kano.

To sai dai bayan kamo shi da aka yi bisa umarnin Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano, CP Salman Dogo Garba, an gano kayan ‘Yan Sanda hudu a gidansa, a inda daga bisani ya tabbatar da cewa yana ta’ammali da kayan maye.

domin haka ne CP Dogo Garba ya ce ba zasu dagawa masu aikata sojan gona da sunan rundunar ko kuma ‘Yan Sandan Sarauniya ba domin haka rundunar ta bayar da wannan lambar waya (07038188127), domin al’umma su shigar da korafi akan ‘Yan Sandan dake musguna musu.

A karshe rundunar ta kuma bada lambobin wayar da za’a bada rahoton dukkan wani abu da ba’a gamsu da shi ba, 08032419754, 08123821575.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp