Home Labarai Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta Kama Dan Sandan Bogi a jihar

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta Kama Dan Sandan Bogi a jihar

Rundunar  ‘yan sandna jihar kano ta sami nasarar kama wani matashi da take zargin da yin sojan gona, matsayin dan sandan bodi a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da Kakakin rundunar na kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar aka rabawa manema labarai a jihar a daren Alhamis, inda ya ce sun kama shi ne biyo bayan koken da al’umma suke yi a Kansa.

A cewar Kiyawa, “Mun kama wani matashin Salisu Bala mazaunin unguwar Kurna, a sakamakon yadda yake sojan gona da kakin ‘Yan Sanda yana karbar kudi a hannun al’umma da sunan shi Dan Sandan Sarauniya ne”.

Kuma dai yana gudanar da wannan aika-aikar tasa ne a unguwannin Sabon Gari, Fagge, Koki dake kwaryar birnin Kano.

To sai dai bayan kamo shi da aka yi bisa umarnin Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano, CP Salman Dogo Garba, an gano kayan ‘Yan Sanda hudu a gidansa, a inda daga bisani ya tabbatar da cewa yana ta’ammali da kayan maye.

domin haka ne CP Dogo Garba ya ce ba zasu dagawa masu aikata sojan gona da sunan rundunar ko kuma ‘Yan Sandan Sarauniya ba domin haka rundunar ta bayar da wannan lambar waya (07038188127), domin al’umma su shigar da korafi akan ‘Yan Sandan dake musguna musu.

A karshe rundunar ta kuma bada lambobin wayar da za’a bada rahoton dukkan wani abu da ba’a gamsu da shi ba, 08032419754, 08123821575.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp