Home Labarai Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta Kama Dan Sandan Bogi a jihar

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta Kama Dan Sandan Bogi a jihar

Rundunar  ‘yan sandna jihar kano ta sami nasarar kama wani matashi da take zargin da yin sojan gona, matsayin dan sandan bodi a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da Kakakin rundunar na kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar aka rabawa manema labarai a jihar a daren Alhamis, inda ya ce sun kama shi ne biyo bayan koken da al’umma suke yi a Kansa.

A cewar Kiyawa, “Mun kama wani matashin Salisu Bala mazaunin unguwar Kurna, a sakamakon yadda yake sojan gona da kakin ‘Yan Sanda yana karbar kudi a hannun al’umma da sunan shi Dan Sandan Sarauniya ne”.

Kuma dai yana gudanar da wannan aika-aikar tasa ne a unguwannin Sabon Gari, Fagge, Koki dake kwaryar birnin Kano.

To sai dai bayan kamo shi da aka yi bisa umarnin Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano, CP Salman Dogo Garba, an gano kayan ‘Yan Sanda hudu a gidansa, a inda daga bisani ya tabbatar da cewa yana ta’ammali da kayan maye.

domin haka ne CP Dogo Garba ya ce ba zasu dagawa masu aikata sojan gona da sunan rundunar ko kuma ‘Yan Sandan Sarauniya ba domin haka rundunar ta bayar da wannan lambar waya (07038188127), domin al’umma su shigar da korafi akan ‘Yan Sandan dake musguna musu.

A karshe rundunar ta kuma bada lambobin wayar da za’a bada rahoton dukkan wani abu da ba’a gamsu da shi ba, 08032419754, 08123821575.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp