Home General Janye tsare-tsaren Tinubu zai kawo cikas ga Najeriya – Bankin Duniya

Janye tsare-tsaren Tinubu zai kawo cikas ga Najeriya – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya yi gargaɗin cewa muddin gwamnatin tarayya ta janye tsare-tsaren tattalin arziki da ta fara, to hakan zai iya janyo babbar cikas ga Najeriya.

Babban wakilin bankin a Najeriya, Dr Ndiame Diop, shi ya yi wannan gargaɗi ranar Alhamis a Abuja yayin kaddamar da wani rahoto kan ‘Cigaban Najeriya da kuma ɗorewarta’ a daidai lokacin da ƙasar ke fuskantar matsaloli.

Diop ya ce dole ne a ɓullo da tsare-tsaren domin ɗorewar Najeriya, duk da cewa za su janyo tsadar rayuwa da kuma wahalhalu ga ƴan ƙasar.

“Janye waɗannan tsare-tsare zai jefa Najeriya cikin barazana da kuma tawayar tattalin arziki,” in ji Diop.

Ya ce ƙarin kuɗaɗen shiga da gwamnatin tarayya ta samu a watannin farko na wannan shekara ya faru ne sakamakon cire tallafin man fetur da na kuma na canjin kuɗin waje, inda ya ce hakan ya nuna dole ne a ci gaba da tsare-tsaren.

Tun a lokacin rantsuwar kama aiki ne, shugaba Bola Tinubu ya sanar da janye tallafin man fetur, abin da ya jefa ƴan Najeriya da dama cikin kunci da wahalhalu musamman ma masu karamin karfi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp