Home General Janye tsare-tsaren Tinubu zai kawo cikas ga Najeriya – Bankin Duniya

Janye tsare-tsaren Tinubu zai kawo cikas ga Najeriya – Bankin Duniya

Bola Ahned Tinubu

Bankin Duniya ya yi gargaɗin cewa muddin gwamnatin tarayya ta janye tsare-tsaren tattalin arziki da ta fara, to hakan zai iya janyo babbar cikas ga Najeriya.

Babban wakilin bankin a Najeriya, Dr Ndiame Diop, shi ya yi wannan gargaɗi ranar Alhamis a Abuja yayin kaddamar da wani rahoto kan ‘Cigaban Najeriya da kuma ɗorewarta’ a daidai lokacin da ƙasar ke fuskantar matsaloli.

Diop ya ce dole ne a ɓullo da tsare-tsaren domin ɗorewar Najeriya, duk da cewa za su janyo tsadar rayuwa da kuma wahalhalu ga ƴan ƙasar.

“Janye waɗannan tsare-tsare zai jefa Najeriya cikin barazana da kuma tawayar tattalin arziki,” in ji Diop.

Ya ce ƙarin kuɗaɗen shiga da gwamnatin tarayya ta samu a watannin farko na wannan shekara ya faru ne sakamakon cire tallafin man fetur da na kuma na canjin kuɗin waje, inda ya ce hakan ya nuna dole ne a ci gaba da tsare-tsaren.

Tun a lokacin rantsuwar kama aiki ne, shugaba Bola Tinubu ya sanar da janye tallafin man fetur, abin da ya jefa ƴan Najeriya da dama cikin kunci da wahalhalu musamman ma masu karamin karfi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp