Home General Ambaliya: Gwamnatin Najeriya ta gargaɗi mutane su tashi daga bakin koguna

Ambaliya: Gwamnatin Najeriya ta gargaɗi mutane su tashi daga bakin koguna

Hukumar Kula da Albarkatun Ruwa ta Najeriya (NIHSA), ta ta shawarci ƴan Najeriya da ke zaune a gaɓar tekuna da su bar yankunan cikin gaggawa.

Darakta-janar na hukumar, Umar Mohammed ne ya yi wannan gargaɗi a wata sanarwa, inda ya ce ruwan da ke tekun Benue ya kai matakin ambaliya saboda ƙaruwar mamakon ruwan sama.

Ya kuma buƙaci mutanen da ke zaune a gaɓar tekun Neja da su ma su bar yankin, inda ya ce hukumomin madatsun ruwa na Kainji da Jebba na aikin kare afkuwar ambaliya.

Mohammed ya yi kira ga ƴan Najeriya da su bayar da haɗin-kai ga hukumomin agaji domin ganin an rage barazanar ambaliya.

A baya-bayan nan, gwamnati ta gargaɗi ƴan Najeriya da su tashi daga wuraren da ke da haɗarin afkawa cikin ambaliya sakamakon sake ruwan madatsar Lagdo daga Kamaru.

Wannan ya zo ne bayan mummunar ambaliya da aka fuskanta a Maiduguri sakamakon ɓallewar madatsar ruwa ta Alau wanda ya kashe mutane 37 tare da ɗaiɗaita miliyoyi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp