Home General Ambaliya: Gwamnatin Najeriya ta gargaɗi mutane su tashi daga bakin koguna

Ambaliya: Gwamnatin Najeriya ta gargaɗi mutane su tashi daga bakin koguna

Hukumar Kula da Albarkatun Ruwa ta Najeriya (NIHSA), ta ta shawarci ƴan Najeriya da ke zaune a gaɓar tekuna da su bar yankunan cikin gaggawa.

Darakta-janar na hukumar, Umar Mohammed ne ya yi wannan gargaɗi a wata sanarwa, inda ya ce ruwan da ke tekun Benue ya kai matakin ambaliya saboda ƙaruwar mamakon ruwan sama.

Ya kuma buƙaci mutanen da ke zaune a gaɓar tekun Neja da su ma su bar yankin, inda ya ce hukumomin madatsun ruwa na Kainji da Jebba na aikin kare afkuwar ambaliya.

Mohammed ya yi kira ga ƴan Najeriya da su bayar da haɗin-kai ga hukumomin agaji domin ganin an rage barazanar ambaliya.

A baya-bayan nan, gwamnati ta gargaɗi ƴan Najeriya da su tashi daga wuraren da ke da haɗarin afkawa cikin ambaliya sakamakon sake ruwan madatsar Lagdo daga Kamaru.

Wannan ya zo ne bayan mummunar ambaliya da aka fuskanta a Maiduguri sakamakon ɓallewar madatsar ruwa ta Alau wanda ya kashe mutane 37 tare da ɗaiɗaita miliyoyi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp