Home General Gwamnatin Kano ta tallafawa wadanda gobara ta shafa a jihar Jigawa

Gwamnatin Kano ta tallafawa wadanda gobara ta shafa a jihar Jigawa

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya tallafawa mutanen da iftila’in fashewar tankar mai ya shafa a garin Majiya dake karamar hukumar Taura a jihar Jigawa da kyautar naira miliya 100.

Gwamnan ya bada tallafin ne lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya da jaje ga al’ummar jihar Jigawa bisa wannan ibtila’i wanda ya yi sanadiyyar rasa rayuka sama da 160 da kuma jikkata al’umma da dama.

Gwamna Abba ya miƙa ta’aziyyarsa a madadin gwamnati da al’ummar jihar Kano tare da fatan Allah ya kare afkuwar hakan a nan gaba.

Har ila yau gwamnan ya ƙara da cewa ibtila’in ba iya al’ummar jihar jigawa kaɗai ya shafa ba, har ma da al’umar jihar Kano, la’akari da dangantakar dake tsakanin jihohin biyu.

Daga nan ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suku rigamu gidan gaskiya ya bawa waɗanda suka jikkata lafiya.

A nasa bangaren, gwamnan jihar Jigawa Alhaji Umar Namadi Ɗanmoɗi ya godewa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa ziyarar jaje da ta’aziyyar da ya kaiwa al’ummar jihar, inda ya ce ziyarar zata kara karfafa dangantakar dake tsakanin jihohin biyu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp