Home General Gwamnatin Kano ta tallafawa wadanda gobara ta shafa a jihar Jigawa

Gwamnatin Kano ta tallafawa wadanda gobara ta shafa a jihar Jigawa

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya tallafawa mutanen da iftila’in fashewar tankar mai ya shafa a garin Majiya dake karamar hukumar Taura a jihar Jigawa da kyautar naira miliya 100.

Gwamnan ya bada tallafin ne lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya da jaje ga al’ummar jihar Jigawa bisa wannan ibtila’i wanda ya yi sanadiyyar rasa rayuka sama da 160 da kuma jikkata al’umma da dama.

Gwamna Abba ya miƙa ta’aziyyarsa a madadin gwamnati da al’ummar jihar Kano tare da fatan Allah ya kare afkuwar hakan a nan gaba.

Har ila yau gwamnan ya ƙara da cewa ibtila’in ba iya al’ummar jihar jigawa kaɗai ya shafa ba, har ma da al’umar jihar Kano, la’akari da dangantakar dake tsakanin jihohin biyu.

Daga nan ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suku rigamu gidan gaskiya ya bawa waɗanda suka jikkata lafiya.

A nasa bangaren, gwamnan jihar Jigawa Alhaji Umar Namadi Ɗanmoɗi ya godewa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa ziyarar jaje da ta’aziyyar da ya kaiwa al’ummar jihar, inda ya ce ziyarar zata kara karfafa dangantakar dake tsakanin jihohin biyu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp