Home General EFCC za ta sa ido kan kashe kuɗaɗen ƙananan hukumomi

EFCC za ta sa ido kan kashe kuɗaɗen ƙananan hukumomi

Hukumar EFCC ta ce za ta ƙarfafa bibiya tare da bin diddigin yadda ƙananan hukumomi suke kashe kuɗaɗensu a daidai lokacin da ake tunanin cin gashin kansu zai fara aiki daga watan Nuwamba, inda ake tunanin za a fara tura musu kuɗadensu kai-tsaye.

Tura kuɗaɗen kai-tsaye na cikin yunƙurin tabbatar da cin gashin kan ƙananan hukumomin guda 774 a Najeriya, lamarin da shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi na Najeriya, Hakeem Ambaliya ya bayyana wa jaridar Punch cewa suna farin ciki.

A ranar 11 ga watan Yulin bana ne dai Kotun Ƙolin Najeriya, ƙarƙashin jagorancin Mai shari’a Garba Lawal, ta yanke hukuncin cewa ba daidai ba ne gwamnoni su riƙa karɓa tare da kula da kuɗaɗen ƙananan hukumomi, inda ta buƙaci akanta-janar na ƙasar ya tabbatar ana tura wa ƙananan hukumomin kuɗaɗensu kai-tsaye.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp