Home General Kwankwaso ya magantu kan matsalar wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

Kwankwaso ya magantu kan matsalar wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana rashin jin daɗinsa kan rashin wutar lantar a mafi yawan jihohin Arewa.

Kamar yadda ya rubuta a shafinsa na X, Kwankwaso ya ce, “Abin takaici ne a ce mafi yawan yankunan Arewa suna zaune cikin duhun rashin wutar lantarki saboda tangarɗa a layin lantarkin 330kV wanda ya ɗauko wuta daga Shiroro zuwa Kaduna, wanda shi ne yake ba jihohin Kano da Kaduna, da layin da yake ba Bauchi da Gombe da wasu jihohin arewa maso gabas wuta.

“Matsalar ta ƙara ta’azzara ne saboda yanayin tsadar man fetur da ake ciki a Najeriya, wanda ya tilasta wa kamfanoni da kasuwanci da dama suka durƙushe.

Sannan lokacin da aka ɗauka ba a magance matsalar ba, ya nuna cewa akwai matsala a ɓangaren makamashin Najeriya,” in ji shi, inda ya ƙara da cewa akwai buƙatar a ɗauki mataki domin guje wa sake aukuwar lamarin, ta hanyar nemo wasu hanyoyin makamashin.

“Ina ba jihohin da ƴan kasuwa shawarar su zuba kuɗi a wasu hanyoyin samar da makamashin domin rage ta’allaƙa da hanyar makamashi guda ɗaya,” in ji Kwankwaso.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp